Home General Mutum 8 Sun Mutu a rikicin kabilanci a Sudan

Mutum 8 Sun Mutu a rikicin kabilanci a Sudan

Jami’an agaji a yankin Darfur na ƙasar Sudan sun ce akalla mutane takwas ne suka mutu a rikicin da ya ɓarke a cikin dare tsakanin wasu al’ummomin da ke zaman doya da manja.

Da farko dai an fara harbe-harbe ne a garin Zalingei, daga bisani ‘yan kabilar Rizeigat ta Larabawa, da suka kai hari wani sansanin ‘yan gudun hijira na ‘yan kabilar Fur, a kan babura.

Ɓarkewar tashe-tashen hankula sun karu tun bayan janyewar tawagar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya a bara.

Har yanzu dai yankin na Darfur bai farfaɗo ba daga yaƙin da ya sha fama da shi tun kusan shekaru ashirin da suka gabata, wanda ya raba sama da mutane miliyan biyu da gidajensu.

Ana zargin da sa hannun wasu mayakan sa kai da ke samun goyon bayan gwamnati a wasu hare-haren da ake kaiwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp