Home General Mutum 8 Sun Mutu a rikicin kabilanci a Sudan

Mutum 8 Sun Mutu a rikicin kabilanci a Sudan

Jami’an agaji a yankin Darfur na ƙasar Sudan sun ce akalla mutane takwas ne suka mutu a rikicin da ya ɓarke a cikin dare tsakanin wasu al’ummomin da ke zaman doya da manja.

Da farko dai an fara harbe-harbe ne a garin Zalingei, daga bisani ‘yan kabilar Rizeigat ta Larabawa, da suka kai hari wani sansanin ‘yan gudun hijira na ‘yan kabilar Fur, a kan babura.

Ɓarkewar tashe-tashen hankula sun karu tun bayan janyewar tawagar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya a bara.

Har yanzu dai yankin na Darfur bai farfaɗo ba daga yaƙin da ya sha fama da shi tun kusan shekaru ashirin da suka gabata, wanda ya raba sama da mutane miliyan biyu da gidajensu.

Ana zargin da sa hannun wasu mayakan sa kai da ke samun goyon bayan gwamnati a wasu hare-haren da ake kaiwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp