Home General Nijeriya na da kwararrun likitocin Koda 250 kawai

Nijeriya na da kwararrun likitocin Koda 250 kawai

Wani kwararren likitan koda a cibiyar lura da cutar koda ta Zenith dare birnin Abuja a Nijeriya, Dakta de faponle, ya bayyana cewa kasar nada kwararrun likitocin a fannin cutar koda 250.

Faponle ya bayyana hakan ne ranar laraba a birnin Ilorin yayin da yake gabatar da wata Makala a babban taron kimiyya na shekara-shekara da kungiyar likitoci masu neman kwarewa suka shirya a jami’ar Ilorin (ARD-UITH).

Masani yayi magane kan “kariyar koda: yadda cutar ke kara kamari, tare da kira domin daukar mataki.

ya koka bisa karancin kwararru a fannin lalura ta koda a fadin kasar, inda ya kara da cewa  sun yi kadan su iya lura da wadanda ke dauke da cutar a fadin Nijeriya.

Ya bayyana lalura ta koda matsayin cuta ta biyar dake assasa mutuwa a fadin duniya, wadda ke jan ragamar matsalolin lafiya a duniya.

“kaso daya ciki 8 na Al’ummar duniya nada matsalar koda, dukkan namiji daya cikin biyar na dauke da cutar, yayin damace daya cikin 4 ke dauke da cutar,” kamar yadda yace.

Faponle ya bayyana cutar ta koda matsayin cutar dake haba da kadan-kadan, wadda ke dakile koda wajen gudanar da aikinta yadda ya kamata a cikin shekaru da dama abinda ke kai ga lalacewar ta baki daya.

Ya kuma jaddada muhimmancin koda cikin gabban dan adam na yadda take aikin tace guda da abubuwa maras kyau daga cikin dan Adam.

“ana kallon ta matsayin gama mafi amfani a jikin dan Adam, wadda take tace jini har sau Arba’in a rana daya. Babu wata wani mashin da ai iya yin wannan aiki,” a cewar sa.

Ya kara da cewa sun fahimci mutanen dake dauke da cuta ta koda basa fahimtar suna dauke da ita doin alamun fasa bayyana a farko-farkon cutar.

Daga bisani yayi gargadi kan masu yawan ta’ammali da magungunan gargajiya, dasu guji yin hakan, tare da yawaita shawo kan hawan jini da ciwon siga.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp