Home General Nijeriya na da kwararrun likitocin Koda 250 kawai

Nijeriya na da kwararrun likitocin Koda 250 kawai

Wani kwararren likitan koda a cibiyar lura da cutar koda ta Zenith dare birnin Abuja a Nijeriya, Dakta de faponle, ya bayyana cewa kasar nada kwararrun likitocin a fannin cutar koda 250.

Faponle ya bayyana hakan ne ranar laraba a birnin Ilorin yayin da yake gabatar da wata Makala a babban taron kimiyya na shekara-shekara da kungiyar likitoci masu neman kwarewa suka shirya a jami’ar Ilorin (ARD-UITH).

Masani yayi magane kan “kariyar koda: yadda cutar ke kara kamari, tare da kira domin daukar mataki.

ya koka bisa karancin kwararru a fannin lalura ta koda a fadin kasar, inda ya kara da cewa  sun yi kadan su iya lura da wadanda ke dauke da cutar a fadin Nijeriya.

Ya bayyana lalura ta koda matsayin cuta ta biyar dake assasa mutuwa a fadin duniya, wadda ke jan ragamar matsalolin lafiya a duniya.

“kaso daya ciki 8 na Al’ummar duniya nada matsalar koda, dukkan namiji daya cikin biyar na dauke da cutar, yayin damace daya cikin 4 ke dauke da cutar,” kamar yadda yace.

Faponle ya bayyana cutar ta koda matsayin cutar dake haba da kadan-kadan, wadda ke dakile koda wajen gudanar da aikinta yadda ya kamata a cikin shekaru da dama abinda ke kai ga lalacewar ta baki daya.

Ya kuma jaddada muhimmancin koda cikin gabban dan adam na yadda take aikin tace guda da abubuwa maras kyau daga cikin dan Adam.

“ana kallon ta matsayin gama mafi amfani a jikin dan Adam, wadda take tace jini har sau Arba’in a rana daya. Babu wata wani mashin da ai iya yin wannan aiki,” a cewar sa.

Ya kara da cewa sun fahimci mutanen dake dauke da cuta ta koda basa fahimtar suna dauke da ita doin alamun fasa bayyana a farko-farkon cutar.

Daga bisani yayi gargadi kan masu yawan ta’ammali da magungunan gargajiya, dasu guji yin hakan, tare da yawaita shawo kan hawan jini da ciwon siga.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp