Home General Wasu Sabbin Hare-Haren ‘Yan Bindiga a Jihohin Sokoto da Katsina sun yi...

Wasu Sabbin Hare-Haren ‘Yan Bindiga a Jihohin Sokoto da Katsina sun yi sandiyyar Mutuwar Mutane 13 tare da garkuwa da 73

‘Yan bindiga sun sake hallaka mutane 14, tare da yin garkuwa da 18 a jihohin Sokoto da Katsina dake arewa maso yammacin Nijeriya.

A gabashin jihar Sokoto , an hallaka mutane 13 tare da yin garkuwa da 73 wanda suka hadar da mata da kananan yara.

Hare-haren ya auku a kauyuka mabanbamta, da suka hadar da sabon birni, gada da kuma yankunan karamar hukumar Goronyo.

Jaridar daily ta ruwato cewa an dukkan hare-haren an kai su ne a lokaci gusa ranar litinin din makoon daya gabata.

Da yake tattaunawa da jaridar wani mai rike da sarautar gargajiya a sabon birin, wanda ya bukaci a sakaye sunan sa, ya ce kauyuka 3 mayakan suka kaiwa hari a karamar hukumar sa inda suka hallaka mutane 11.

Kauyukan sun hadar da gatawa da Dangari inda mutane 6 suka mutu, 2 a gatawa 3 kuma a kurawa.

Shugaban jami’an sa kai na Vijilanti a sabonda birni, Musa Muhammad da Dan Majalisa ma wakiltar sabon birnin a zauren majalisar wakilai Mustapha Boza, dake wakiltar Sabon birni ta kudu su bayyana cewa dukkan  mutanen an halaka su ne a gona ranar litinin da karfe 5 na yamma.

Boza yace sun kuma yi garkuwa da mutane da dama yayi da suka kai harin.

Haka kuma shugaban karamar hukumar Goronyo, Abdulwahab Goronyo, wand aya koka bisa harin yace maharani sun hallaka mutane 23, yayin da suka yi garkuwa da sauran a garuruwan shinkafi da  kagara a ranar litinin din data gabata.

shima Dan majalisa mai wakiltar mazabar Gada ta gabas a zauren majalisar jiha, Kabiru dauda, ya bayyana cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane sama da 50 da suka hadar da mata da kananan yara a ranar litinin a yankin.

“bazan iya fada maka takamaiman adadin mutanen da aka sace ba, amma da yawan mutanen mun sun samin raukana, amma dai suka samun kulawar likitoci a asibitocin daban-daban. Kamar yadda ya bayyana.

Dauda ya hakikance cewa duk da korafe-korafen da Al’ummar ke yi bisa harin rashin  tsaron da suke ciki, kawo yanzu babu wani matakin da aka dauka domin magance matsalar ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp