Home General Wasu Sabbin Hare-Haren ‘Yan Bindiga a Jihohin Sokoto da Katsina sun yi...

Wasu Sabbin Hare-Haren ‘Yan Bindiga a Jihohin Sokoto da Katsina sun yi sandiyyar Mutuwar Mutane 13 tare da garkuwa da 73

‘Yan bindiga sun sake hallaka mutane 14, tare da yin garkuwa da 18 a jihohin Sokoto da Katsina dake arewa maso yammacin Nijeriya.

A gabashin jihar Sokoto , an hallaka mutane 13 tare da yin garkuwa da 73 wanda suka hadar da mata da kananan yara.

Hare-haren ya auku a kauyuka mabanbamta, da suka hadar da sabon birni, gada da kuma yankunan karamar hukumar Goronyo.

Jaridar daily ta ruwato cewa an dukkan hare-haren an kai su ne a lokaci gusa ranar litinin din makoon daya gabata.

Da yake tattaunawa da jaridar wani mai rike da sarautar gargajiya a sabon birin, wanda ya bukaci a sakaye sunan sa, ya ce kauyuka 3 mayakan suka kaiwa hari a karamar hukumar sa inda suka hallaka mutane 11.

Kauyukan sun hadar da gatawa da Dangari inda mutane 6 suka mutu, 2 a gatawa 3 kuma a kurawa.

Shugaban jami’an sa kai na Vijilanti a sabonda birni, Musa Muhammad da Dan Majalisa ma wakiltar sabon birnin a zauren majalisar wakilai Mustapha Boza, dake wakiltar Sabon birni ta kudu su bayyana cewa dukkan  mutanen an halaka su ne a gona ranar litinin da karfe 5 na yamma.

Boza yace sun kuma yi garkuwa da mutane da dama yayi da suka kai harin.

Haka kuma shugaban karamar hukumar Goronyo, Abdulwahab Goronyo, wand aya koka bisa harin yace maharani sun hallaka mutane 23, yayin da suka yi garkuwa da sauran a garuruwan shinkafi da  kagara a ranar litinin din data gabata.

shima Dan majalisa mai wakiltar mazabar Gada ta gabas a zauren majalisar jiha, Kabiru dauda, ya bayyana cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane sama da 50 da suka hadar da mata da kananan yara a ranar litinin a yankin.

“bazan iya fada maka takamaiman adadin mutanen da aka sace ba, amma da yawan mutanen mun sun samin raukana, amma dai suka samun kulawar likitoci a asibitocin daban-daban. Kamar yadda ya bayyana.

Dauda ya hakikance cewa duk da korafe-korafen da Al’ummar ke yi bisa harin rashin  tsaron da suke ciki, kawo yanzu babu wani matakin da aka dauka domin magance matsalar ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp