Wata gobara ta tashi a kasuwar da ake kira Kasuwar Litinin da ke birnin Maiduguri.
Gobarar, wadda rahotanni suka ce ta tashi ne a daren jiya ta yi ɓarnar da har yanzu ba a tantance ba.
Read Also:
- Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar Shekara
- Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta’addanci
- Binciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?
Hotunan bidiyo da aka wallafa a shafukan sada zumunta sun nuna yadda hayaƙi ya turnuƙe sararin samaniyar birnin na Maiduguri sanadiyyar gobarar.
Ganau sun tabbatarwa da PRNigeria cewa wutar dai ta tashi da misalin karfe 2 na daren lahadi inda daga bisani ta yadu a sassan kasuwar.
PRNigeria hausa










