Home General Muna sane da matsalolin da ake samu a rumfunan zabe-INEC

Muna sane da matsalolin da ake samu a rumfunan zabe-INEC

Shugaban hukumar zaɓen Najeriya (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu ya ce hukumar na lura tare da sanya ido game da yadda zaɓe ke gudana a faɗin ƙasar.

Ya ce hukumar ta samu rahotonnin wasu ‘yan matsaloli nan da can, to sai dai hukumar a shirye take wajen magance matsalolin.

A yau ne dai hukumar ke gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar dokokin tarayya.

Farfesa Mahmud ya ƙara da cewa burin hukumar shi ne tabbatar da samun sahihi da ingantaccen zaben a ƙasar.

Farfesa Yakubu ya ce wannan shi ne karo na farko da hukumar ke gudanar da zaɓen kamar yadda aka tsara ba tare da ɗage zaɓen ba.

Ya ce ana ci gaba da zaɓe a faɗin ƙasar, kuma na’urar BVAS da ake amfani da ita tana aiki yadda ya kamata a wurare da dama a faɗin kasar.

Ya ce rahotonnin da hukumar ke samu daga ofisoshin hukumar na jihohi da birnin tarayya na nuna cewa ƙorafe-ƙorafen da jama’a ke yi game da aikin na’urar BVAS na ci gaba da raguwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp