Home General Muna sane da matsalolin da ake samu a rumfunan zabe-INEC

Muna sane da matsalolin da ake samu a rumfunan zabe-INEC

Shugaban hukumar zaɓen Najeriya (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu ya ce hukumar na lura tare da sanya ido game da yadda zaɓe ke gudana a faɗin ƙasar.

Ya ce hukumar ta samu rahotonnin wasu ‘yan matsaloli nan da can, to sai dai hukumar a shirye take wajen magance matsalolin.

A yau ne dai hukumar ke gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar dokokin tarayya.

Farfesa Mahmud ya ƙara da cewa burin hukumar shi ne tabbatar da samun sahihi da ingantaccen zaben a ƙasar.

Farfesa Yakubu ya ce wannan shi ne karo na farko da hukumar ke gudanar da zaɓen kamar yadda aka tsara ba tare da ɗage zaɓen ba.

Ya ce ana ci gaba da zaɓe a faɗin ƙasar, kuma na’urar BVAS da ake amfani da ita tana aiki yadda ya kamata a wurare da dama a faɗin kasar.

Ya ce rahotonnin da hukumar ke samu daga ofisoshin hukumar na jihohi da birnin tarayya na nuna cewa ƙorafe-ƙorafen da jama’a ke yi game da aikin na’urar BVAS na ci gaba da raguwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 
X whatsapp