Home General An kai hare-hare 60 a lokacin yakin neman zaɓe – CDD

An kai hare-hare 60 a lokacin yakin neman zaɓe – CDD

Akalla hare-hare 60 aka kai tare kuma da kashe mutum tara a lokacin yakin neman zaɓe a faɗin Najeriya gabanin zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya da za a gudanar a ranar Asabar.

Cibiyar Tabbatar da Dimokuraɗiyya da Ci Gaba CDD, ce ta bayyana hakan a cikin wani rahoto da ta fitar gabanin shiga rumfunan zabe domin kaɗa kuri’a, inda ta ce wasu da dama kuma sun jikkata a hare-haren da aka kai tun fara yakin neman zaɓe a watan Satumban 2022.

CDD ta ce batun rashin tsaro da ƙarancin man fetur da na kuɗi da kuma sauran abubuwa za su iya kawo cikas ga yadda zaɓen zai gudana.

“A karshen shekarar 2022, rikice-rikicen da ke da alaƙa da siyasa sun ƙaru tun bayan zaɓen 2019 da aa gudanar. Alkaluman da muka tattara ya nuna cewa an kai hari sau 60 a lokacin yakin neman zaɓe, inda mutum tara suka mutu,” in ji CDD.

Kungiyar ta kuma nuna damuwa kan yadda ta ce ‘yan siyasa na ɗaukar ‘yan bangar siyasa domin kawo cikas a zaɓen da za a gudanar, inda ta ce hakan zai ƙara janyo taɓarɓarewar matsalar tsaro.

Cibiyar ta yi kira jam’iyyun siyasa da su tabbatar da cewa mambobin da kuma magoya bayansu sun bi sahun sharuɗan da aka kwamitin zaman lafiya ya zartas yayin lokacin saka hannu a yarjejeniyar yin zaɓe lami lafiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp