Home General Za’a Rufe Iyakokin Nijeriya saboda Zabe-NIS

Za’a Rufe Iyakokin Nijeriya saboda Zabe-NIS

Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe iyakokin ƙasar na sa’a 24 gabanin babban zaɓen ƙasar da ke tafe a ranar Asabar.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Hukumar Shige da Fice ta Najeriya ta wallafa a shafinta na tiwita wanda ya samu sa hannun shugabanta, Isah Jere Idris.

Sanarwar ta ce daga ranar Asabar za a rufe dukkan iyakokin ƙasar na ƙasa har zuwa ranar Lahadi 26 ga watan Febrairun 2023.

Idris Jere ya buƙaci dukkan shugabannin hukumar da ke kan iyakoki da su tabbatar an bi sahun wannan umarni.

Ya ce hukumar a shirye take wajen ganin ta bayar da gudummawa na ganin an gudanar da zaɓukan ƙasar lami lafiya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSF
X whatsapp