Home General EFCC ta ce ta kai jami’anta wuraren zaɓe domin sanya ido kan...

EFCC ta ce ta kai jami’anta wuraren zaɓe domin sanya ido kan ayyukan zaɓen 2023

Hukumar yaƙi da yi wa tattalin arziƙin ƙasa ta’annati EFCC ta ce ta kai jami’anta wuraren zaɓe domin sanya ido kan ayyukan zaɓen, ta kuma bayar da lambobin wayar da za a riƙa buga mata domin ko ta kwana.

EFCC ta wallafa haka ne a shafinta na Twitter inda ta bayyana lambobin wayar da za a riƙa kiranta kai tsaye da an ga wani abu mai kama da laifukan kudi a yayin zaɓe.

A wani ɓangare na tabbatar da an yi zaɓukan shugaban ƙasa da na ‘yan majalisa salin alin shi yasa EFCC ta kai ma’aikatan nata.

Tana so ta tabbatar da an yi zaɓen babu cuta babu cutarwa shi yasa za ta sanya ido kan yadda ake sayan kuri’a wani abu da ya zama ruwan dare a siyasar Najeriya, ko kuma bai wa jami’an da ke aiki kuɗi su ɗauke kai a gudanar da wani abu da bai dace ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp