Home General EFCC ta ce ta kai jami’anta wuraren zaɓe domin sanya ido kan...

EFCC ta ce ta kai jami’anta wuraren zaɓe domin sanya ido kan ayyukan zaɓen 2023

Hukumar yaƙi da yi wa tattalin arziƙin ƙasa ta’annati EFCC ta ce ta kai jami’anta wuraren zaɓe domin sanya ido kan ayyukan zaɓen, ta kuma bayar da lambobin wayar da za a riƙa buga mata domin ko ta kwana.

EFCC ta wallafa haka ne a shafinta na Twitter inda ta bayyana lambobin wayar da za a riƙa kiranta kai tsaye da an ga wani abu mai kama da laifukan kudi a yayin zaɓe.

A wani ɓangare na tabbatar da an yi zaɓukan shugaban ƙasa da na ‘yan majalisa salin alin shi yasa EFCC ta kai ma’aikatan nata.

Tana so ta tabbatar da an yi zaɓen babu cuta babu cutarwa shi yasa za ta sanya ido kan yadda ake sayan kuri’a wani abu da ya zama ruwan dare a siyasar Najeriya, ko kuma bai wa jami’an da ke aiki kuɗi su ɗauke kai a gudanar da wani abu da bai dace ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man Kan Sayar da Farashin FeturNECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin Najeriya
X whatsapp