Home Taska Hatsarin Mota ya yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 25 a Bauchi

Hatsarin Mota ya yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 25 a Bauchi

Accident

Hatsarin Mota ya yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 25 a Bauchi

 

Haɗarin ya faru ne akan hanyar Hadeja-Potiskum ta zuwa ƙaramar hukumar Gamawa dake jihar Bauchi.

Direban motar ya rasa yadda zai sarrafa motar ne, wanda hakan yasa ya aukawa wasu mutane 11 dake hutawa a ƙarƙashin wata bishiya.

Hukumar FRSC ta Bauchi tace hatsarin ya faru ne saboda taƙe motar da akayi da kaya masu yawa, da gudun wuce sa’a, da yasa tayar motar ta fashe.

Bauchi- Idan ajali yayi kira ko babu ciwo dole aje. Mutuwa kenan, mai raba bawa da rai, bawai don baya so ba.

Ita mutuwa ko babu ciwo idan lokaci yayi, tafiya akeyi bagatatan.

Mutuwar ita tazo wa wasu mutane kimanin 25 dake tsaka da tafiya akan hanyar su ta Hadeja-Potiskum, dake cikin ƙaramar hukumar Gamawan Jihar Bauchi.

Duk dai a cikin mummunan hatsarin, wasu daga cikin mahayan kimanin guda 10 sun samu munanan raunuka a cikin motar dake tsaka da zabga gudu.

Lamarin maras daɗin ji da gani ya faru ne ranar Alhamis, da misalin ƙarfe 4:30 na yamma.

Kwamandan rundunar kare haɗurra ta ƙasa sashin jihar Bauchi, Yusuf Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin ga Jaridar Punch a safiyar yau juma’a.

Jami’in yace, a cikin mutanen 35 akwai maza 19, mata 11, yara maza guda 2 da kuma yara mata guda uku.

Da jami’in yake zayyana yadda haɗarin ya faru, yace, direban motan da tayi haɗari, ya rasa yadda zai sarrafa motar ne, wanda hakan yasa ya aukawa wasu mutane 11 dake hutawa a ƙarƙashin wata bishiya dake kusa da wajen wankin mota.

Ga yadda Abdullahi, ya zayyana lamarin:

“Kwarai kuwa, an samu mummunan hatsarin mota a Udubo, akan hanyar Hadeja-Potiskum ta zuwa ƙaramar hukumar Gamawa dake jihar Bauchi. Hatsarin ya faru jiya Alhamis, watau 23rd ga watan Maris na 2023.” inji shi.

“Hatsarin ya haɗa da wata motar haya samfurin Toyota Hummer Bus mai lamba ‘JMA 59XA’.”,

“Hatsarin ya faru ne saboda taƙe motar da akayi da kaya masu yawa, gudun wuce sa’a, da yasa tayar motar ta fashe har motar ta ƙasa sarrafuwa.” Inji shi.

Jami’in ya tabbatar da cewa, sun isa wajen ne bayan samun sanarwar faruwar lamarin, inda basui wata wata ba, suka tura jami’an su na ujula domin basu tallafin gaggawa.

Koda suka isa asibiti da masu hatsarin ne aka tabbatar da cewar, mutane 25 sun sheka barzahu yayin da 10 ke ci gaba da amsar magani sakamakon mummunan ciwo da suka ji a jikkunan su.

Gawarwakin wanda suka mutu an ajiye su a dakin ajiye gawa na FMC, Azare.

Daga ƙarshe, bayan jimamin lamarin, jami’in yayi kira ga matuƙa dasu kula sosai wajen bin dokokin tuki, domin rage haɗurra dake sawa a rasa rai da kuma sawa aji ciwo.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp