Home DUNIYA An amince da yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta ta sa’a 24 a Sudan...

An amince da yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta ta sa’a 24 a Sudan – RSF

Dakaru masu sanye da kayan sarki na RSF da ke faɗa da sojojin Sudan sun bayyana amincewa da yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta ta sa’a 24, fara wa da misalin karfe 6 na yamma.

Cikin wata sanarwa da dakarun suka wallafa a shafinta na Twitter, ta ce “Mun amince da kudurin tsagaita buɗe wuta, kuma muna fatan sauran ɓangarorin za su bi yarjejeniyar da aka cimma,” in ji kungiyar

Sai dai babu tabbacin cewa ko sojojin Sudan sun amince da tsagaita buɗe wutan.

Ɓangarorin biyu sun ce za su mutunta yarjejeniyar tsagaita wuta ta sa’o’i 24 a ranar Talata.

Ana dai ci gaba da gwabza kazamin faɗa a ƙasar ta Sudan, musamman a kusa da hedkwatar sojojin da ke tsakiyar birnin Khartoum.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp