Home Labarai Gwamnan jihar kano ya cire kuɗin makarantar Gidan kangararro ta Kiru

Gwamnan jihar kano ya cire kuɗin makarantar Gidan kangararro ta Kiru

Gwamnan jihar kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya yi alkawarin gyarawa da inganta cibiyar gyaran hali da tarbiyya deke karamar hukumar Kiru domin magance matsalolin shaye-shaye da matasa ke yi a jihar kano.

Gwamnan ya bayyana hakan ne lokacin da ya ziyarci cibiyar domin ganin matsalolin da take fuskanta da kuma duba yadda za’a magance su.

Gwamnan yace gwamnatin sa zata Maida hankali wajen inganta rayuwar matasa domin su ne kashin bayan cigaban al’umma.

Yace shaye-shayen miyagun kwayoyi shi ke haddasa matsaloli na ta’addanci rashin tsaro da saura laifuffuka a cikin al’umma, a don haka yace zai inganta cibiyar ta hanyar samar da ababen more rayuwa da Kuma abincin da matasan dake gidan zasu rika ci.

Wannan ziyarana matsayin aikin Gwamnan na farko bayan rantsar da shi , yace gwamnati ta daukewa Iyayen da yaransu suke karɓar horo, tare da umartar Babbar Sakatariyar ta ma’aikatar mata da ta rubuto masa matsalolin da cibiyar take fuskanta domin magance wa nan da wata guda.

Da take nata jawabin Babbar Sakatariyar ma’aikatar mata ta jihar kano Dr. Sa’adatu Sa’idu Bala ta godewa sabon gwamnan saboda ziyarar da yakai cibiyar wanda tace hakan ya nuna yadda ya damu da halin da matasa ke ciki a jihar kano musamman batun kwacen waya da ake kashe mutane akai.

Babbar Sakatariyar ta bayyana cewa cibiyar tana taka rawa wajen gyara rayuwar matasa ta hanyar basu magani da koya musu sana’o’in dogaro da don inganta rayuwar su. Ta kuma ce cibiyar tana fuskantar matsaloli masu tarin yawa.

Tace ana gudanar da makarantar ne daga Naira 70 da ake biyawa yaran duk wata da kuma Naira dubu dari 5 da tsohuwar gwamnatin kano take ba su.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp