Home Labarai Gwamnan jihar kano ya cire kuɗin makarantar Gidan kangararro ta Kiru

Gwamnan jihar kano ya cire kuɗin makarantar Gidan kangararro ta Kiru

Gwamnan jihar kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya yi alkawarin gyarawa da inganta cibiyar gyaran hali da tarbiyya deke karamar hukumar Kiru domin magance matsalolin shaye-shaye da matasa ke yi a jihar kano.

Gwamnan ya bayyana hakan ne lokacin da ya ziyarci cibiyar domin ganin matsalolin da take fuskanta da kuma duba yadda za’a magance su.

Gwamnan yace gwamnatin sa zata Maida hankali wajen inganta rayuwar matasa domin su ne kashin bayan cigaban al’umma.

Yace shaye-shayen miyagun kwayoyi shi ke haddasa matsaloli na ta’addanci rashin tsaro da saura laifuffuka a cikin al’umma, a don haka yace zai inganta cibiyar ta hanyar samar da ababen more rayuwa da Kuma abincin da matasan dake gidan zasu rika ci.

Wannan ziyarana matsayin aikin Gwamnan na farko bayan rantsar da shi , yace gwamnati ta daukewa Iyayen da yaransu suke karɓar horo, tare da umartar Babbar Sakatariyar ta ma’aikatar mata da ta rubuto masa matsalolin da cibiyar take fuskanta domin magance wa nan da wata guda.

Da take nata jawabin Babbar Sakatariyar ma’aikatar mata ta jihar kano Dr. Sa’adatu Sa’idu Bala ta godewa sabon gwamnan saboda ziyarar da yakai cibiyar wanda tace hakan ya nuna yadda ya damu da halin da matasa ke ciki a jihar kano musamman batun kwacen waya da ake kashe mutane akai.

Babbar Sakatariyar ta bayyana cewa cibiyar tana taka rawa wajen gyara rayuwar matasa ta hanyar basu magani da koya musu sana’o’in dogaro da don inganta rayuwar su. Ta kuma ce cibiyar tana fuskantar matsaloli masu tarin yawa.

Tace ana gudanar da makarantar ne daga Naira 70 da ake biyawa yaran duk wata da kuma Naira dubu dari 5 da tsohuwar gwamnatin kano take ba su.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp