Home Labarai An fara cinkoson sayen fetur a Nijeriya sakamakon kalaman Tinubu

An fara cinkoson sayen fetur a Nijeriya sakamakon kalaman Tinubu

An fara dogayen layuka a gidajen sayar da man fetur da ke birnin Lagos na Najeriya jim kadan da sanarwar da shugaban kasar, Bola Ahmed Tinubu ya yi ta janye kudin tallafin man fetur.

Manema labarai sun rawaito cewa, direbobin motoci sun yi cincirindo a gidajen mai na NNPC da ke Ikeja, inda suke rige-rigen sayen man.

da dama daga cikin gidajen man fetur masu zaman kansu ba sa sayar da man ya zuwa lokacin da fitar da rahoton.

A yayin gabatar da jawabinsa na shan rantsuwar kama aiki a yau Litinin, shugaba Tinubu ya bayyana cewa, mawadata ne kadai ke amfana da kudin tallafin man fetur din a maimakon talakawa.

Tinubu ya ce, gwamnatinsa za ta karkatar da kudin tallafin zuwa ga bangarorin ilimi da lafiya da samar da ayyuka da gina kayayyakin more rayuwa da za su amfani miliyoyin al’umma.

Kazalika shugaban ya ce, zai nazarci korafe-korafe game da dimbin kudaden haraji don ganin an habbaka tattalin arzikin kasar tare da janyo masu zuba jari.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp