Home Labarai Tinubu ya sanya hannu kan dokar bai wa ɗalibai bashi

Tinubu ya sanya hannu kan dokar bai wa ɗalibai bashi

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan dokar bai wa ɗalibai bashin karatu ta ƙasa.

Mai magana da yawun Gwamnatin Tarayya, Dele Alake ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar yau Litinin.

Sanarwar ta ce za a ajiye kuɗaɗen da za a rinƙa bayar da bashin ne a asusun Ma’aikatar Ilimi, kuma ɗaliban manyan makarantu ne kawai za su iya cin gajiyarsu.

Mako biyu da suka gabata ne ƙudirin, wanda shugaban Majalisar Wakilan Tarayya, Femi Gbajabiamila ya gabatar, ya tsallake karatu na uku a Majalisar Dokokin Tarayya.

Dokar za ta bai wa ɗalibai ƴan asalin Najeriya damar karɓar bashi cikin sauƙi, wanda babu ruwa a tattare da shi daga Asusun Bayar da Bashin Karatu na Najeriya.

PRNigeria hausa I

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp