Home Labarai Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu yayi alkawarin rage radadi ga ‘yan kasa

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu yayi alkawarin rage radadi ga ‘yan kasa

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu yayi alkawarin ragewa ‘yan Najeriya radadin cire tallafin man fetur ta hanyar bunkasa bangarorin sufuri, da ababen more rayuwa, da ilimi, da samar da dawwamammen hasken wuta lantarki, da kuma inganta bangaren lafiya.

Shugaba Tinubu yayi wannan alwashi ne lokacin dayake jawabi ga ‘yan Najeriya akan zagayowar ranar dimokradiyya.

Mista Tinubu yacigaba da cewa, ” A ranar demokradiiya ta wannan shekara, Ina kira garemu da mukara sadaukar da kanmu domin karfafa wannan tsari na gwamnati daya baiwa kowa ‘yancinsa, wanda hakan kuma shine tsarinmu tsawon wadannan shekaru 24 da dawowar mulkin demokradiiya.”

A ranar 29 ga watan mayu lokacin dayake jawabi bayan amsar rantsuwa, Shugaba Tinubu yabayyana cire tallafin mai kacokan lamarin daya saka al’ummar kasar cikin rudani biyo bayan tashin gouron zabi da farashin mai da sauran kayan masarufi sukayi a fadin kasar.

Shugaba Tinubu yayi allawarin tabbatar da bai baiwa ‘yan Najeriya kunya ba, tahanyar cika alkawurran daya dauka lokacin yakin neman zabe.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp