Home Labarai Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu yayi alkawarin rage radadi ga ‘yan kasa

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu yayi alkawarin rage radadi ga ‘yan kasa

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu yayi alkawarin ragewa ‘yan Najeriya radadin cire tallafin man fetur ta hanyar bunkasa bangarorin sufuri, da ababen more rayuwa, da ilimi, da samar da dawwamammen hasken wuta lantarki, da kuma inganta bangaren lafiya.

Shugaba Tinubu yayi wannan alwashi ne lokacin dayake jawabi ga ‘yan Najeriya akan zagayowar ranar dimokradiyya.

Mista Tinubu yacigaba da cewa, ” A ranar demokradiiya ta wannan shekara, Ina kira garemu da mukara sadaukar da kanmu domin karfafa wannan tsari na gwamnati daya baiwa kowa ‘yancinsa, wanda hakan kuma shine tsarinmu tsawon wadannan shekaru 24 da dawowar mulkin demokradiiya.”

A ranar 29 ga watan mayu lokacin dayake jawabi bayan amsar rantsuwa, Shugaba Tinubu yabayyana cire tallafin mai kacokan lamarin daya saka al’ummar kasar cikin rudani biyo bayan tashin gouron zabi da farashin mai da sauran kayan masarufi sukayi a fadin kasar.

Shugaba Tinubu yayi allawarin tabbatar da bai baiwa ‘yan Najeriya kunya ba, tahanyar cika alkawurran daya dauka lokacin yakin neman zabe.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp