Home Labarai Gwamnatin Kano zata tabbatar da an aiwatar da duk wasu ayyuka da...

Gwamnatin Kano zata tabbatar da an aiwatar da duk wasu ayyuka da hukumomi masu bada tallafi na kasashen duniya ke aiwatarwa a Kano.

Gwamnatin Kano zata tabbatar da an aiwatar tare da kammala duk wasu ayyuka da hukumomi masu bada tallafi na kasashen duniya ke aiwatarwa a Kano.

Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Engr Abba Kabir Yusuf, ta jaddada kudirinta na bibiyar duk wasu ayyuka da bankin duniya da sauran hukumomi masu bada tallafi ke aiwatarwa a Kano.

Tabbacin hakan ya fito ne ta bakin babban Akanta na Kano Abdulkadir Abdussalam lokacin da yake jagorantar wata ganawa da wakilan kungiyoyi da hukumomin kasashen waje wadanda ke bada tallafi.

Ganawar dai ta hada da dukkanin akantoci dake jihar da kuma masu lura da hukumomin gwamnati.

Abdussalam, ya nuna damuwarsa akan yadda wasu daga cikin ayyukan aka gaza kammalasu wanda hakan ya kawo koma baya a cigaban tattalin arzikin Kano.

Babban Akantan ya buga misali da bangarori irinsu ruwansha da ilimi da lafiya da kuma noma, da yadda kuma suke da alaka takai tsaye da gina dan Adam.

A karshen ganawar, Abdulkadir Abdussalam ya baiwa masu ruwa da tsakin tabbacin gwamnatin Kano na tsayawa tsayin daka domin amfani da tallafin dake shigowa Kano ta hanyar data dace.

Amakon daya gabatane dai Gwamna Abba Kabir Yusuf yanada Abdulkadir Abdussalam amatsayin sabon babban Akantan Kano, kafin nadin nashi dai Darakta ne a hukumar tattara haraji ta jihar Kano.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp