Home Labarai Gwamnatin Kano zata tabbatar da an aiwatar da duk wasu ayyuka da...

Gwamnatin Kano zata tabbatar da an aiwatar da duk wasu ayyuka da hukumomi masu bada tallafi na kasashen duniya ke aiwatarwa a Kano.

Gwamnatin Kano zata tabbatar da an aiwatar tare da kammala duk wasu ayyuka da hukumomi masu bada tallafi na kasashen duniya ke aiwatarwa a Kano.

Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Engr Abba Kabir Yusuf, ta jaddada kudirinta na bibiyar duk wasu ayyuka da bankin duniya da sauran hukumomi masu bada tallafi ke aiwatarwa a Kano.

Tabbacin hakan ya fito ne ta bakin babban Akanta na Kano Abdulkadir Abdussalam lokacin da yake jagorantar wata ganawa da wakilan kungiyoyi da hukumomin kasashen waje wadanda ke bada tallafi.

Ganawar dai ta hada da dukkanin akantoci dake jihar da kuma masu lura da hukumomin gwamnati.

Abdussalam, ya nuna damuwarsa akan yadda wasu daga cikin ayyukan aka gaza kammalasu wanda hakan ya kawo koma baya a cigaban tattalin arzikin Kano.

Babban Akantan ya buga misali da bangarori irinsu ruwansha da ilimi da lafiya da kuma noma, da yadda kuma suke da alaka takai tsaye da gina dan Adam.

A karshen ganawar, Abdulkadir Abdussalam ya baiwa masu ruwa da tsakin tabbacin gwamnatin Kano na tsayawa tsayin daka domin amfani da tallafin dake shigowa Kano ta hanyar data dace.

Amakon daya gabatane dai Gwamna Abba Kabir Yusuf yanada Abdulkadir Abdussalam amatsayin sabon babban Akantan Kano, kafin nadin nashi dai Darakta ne a hukumar tattara haraji ta jihar Kano.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp