Home Labarai Wasu marasa kishin ne ke haifar da matsalolin Daba a – Abba...

Wasu marasa kishin ne ke haifar da matsalolin Daba a – Abba gida-gida

Gwamnan jahar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yaba wa hukumomin tsaron jahar, bisa matakan da suka dauka wajen dakile aiyukan Daba da kuma kwacen wayoyin al’umma a sassan birnin jihar.

Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya bayyana hakan ne a fadar gwamnatin jahar, yayin gabatar da bikin Hawan Nasara a Ranar juma’a.

A cewar gwamnan sun yi kokari wajen hada Kai da jami’an tsaro domin kare rayukan al’umma da dukiyoyinsu, amma duk da haka sai da wasu marasa kishin jahar Kano, wadanda suka dawo da harkar Daba a cikin kwaryar birnin Kano.

“ Mun San su ba wai ba mu San su ba, sun dawo mana da Daba domin basa son cin gaban jahar Kano, kuma basa son zaman lafiya”

Ya Kara da cewa a cikin watan Ramadan da ya gabata, an samu wasu batagarin matasa da suke rubuta wasika su aikata wa Mutane a masallatai, inda suke zuwa tare da farwa Mutane har su Yan yanke su ta Hanyar Daba mu su wukake, sannan kwace mu su wayoyinsu.

“ Ba bu shakka gwamnatin Kano, a karkashin mu ba zata lamunci wannan ta’addanci da ake ba” Gwamnan Kano”.

Gwamnan jahar Kano  Abba Kabir Yusuf, ya godiya wa shugabannin hukumomin tsaron jahar , da suka hada da Kwamishinan Yan sandan jahar CP Muhammed Usaini Gumel, Sojojin Kasa, Sojojin Sama, Hukumar tsaron Farin kaya DSS, hukumar gidan gyaran hali, hukumar kwastam da kuma ta shige da fice da dai sauransu.

Ya ce sun matukar kokarin domin dakile ta’addancin da aka shigo da shi , inda suka bi gida-gida wajen Kano dukkan Wanda aka ji labarin yana aikata ta’addanci , kuma aka gurfanar da su a gaban kotu.

Haka zalika gwamnan ya yi Kira ga mai martaba sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, da su fito tare da hakimansa wajen bayar da gudunmawa don dakile wannan yanayi na ta’addanci.

” bayan an Kai su kotu mutane marasa kishin su suka je kotu, har suka bayar da kudi suka fito da wadanda aka Kama, a saboda haka gwamnatin Kano tana Allah wadai da wannan Abu, kuma su Masu yin hakan ko su Dakata su daina ko kuma gwamnati ta dira akansu” A.K.Y.”.

Ya Kara da cewa gwamnatin jahar Kano tare da hukumomin tsaro da Sarakuna za su Ci gaba da hada Kai, don tabbatar da cewar an ceto al’umma daga halin rashin tabbas da dardar.

” saboda haka mun dau matakai da za mu tabbatar da cewa wannan ta’addanci ya Kau cikin ikon Allah” Abba Kabir “.

Gwamnan ya ce a ko a watannin baya, da fadan Daba ya yi kamari a birnin Kano, sun janyo matasan 222 da suka tuba daga aikata laifuka har gwamnatin kanon, ta ba su sana’o’in dogaro da Kai.

Da yake nasa jawabin mai martaba sarkin Kano, Alhaji Dr. Aminu Ado Bayero, ya bukaci gwamnatin jahar, ta Kara Himma wajen gyaran tarbiyar matasa da kuma yin aiyukan sa za su kawo ci gaban Kano.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp