Home Labarai Gwamnatin tarayya ta kara ranar Alhamis matsayin ranar hutun sallah

Gwamnatin tarayya ta kara ranar Alhamis matsayin ranar hutun sallah

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta ayyana ranar Alhamis 11 ga watan Afrilu, 2024 matsayin Kari cikin ranakun hutu a kasar, a wani bangare na bukukuwan karamar sallah ta shekarar 1445 bayan hijra.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakatariyar ma’aikatar cikin gida Dr. Aishetu Gogo Ndayako.

Sanarwar ta ambaci ministan ma’aikatar Dr. Olubunmi Tunji-Ojo, na taya daukacin Al’ummar Musulmin kasar murnar kamala ibadar azumin watan Ramadan cikin kwanciyar hankali, inda kuma ya bayyana kudirin shugaban kasar Bola Ahmad Tinubu na samawa ‘yan kasar kyakkyawan yanayi.

Idan zamu iya tunawa jaridar PRNigeria ta ambaci ministan ya ayyana ranar talata 9 da kuma 10 ga watan Afrilun, 2024 matsayin ranakun hutun karamar a kasar.

 PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp