Home Labarai Gwamnan Kano ya sake nada Oga Boye a mukami

Gwamnan Kano ya sake nada Oga Boye a mukami

Gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sake yin sabbin nade-nade a cikin kunshin gwamnatin jihar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan yada labaran gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa.

Sanarwar ta ayyana Farfesa Ibrahim Magaji barde matsayin mai bada shawara na musamman ga mai girma gwamna fannin harajin cikin gida.

  1. Dr. Abdulhamid Danladi, mai bawa Gwamnan shawara kan ‘yan kano mazauna ketare na II
  2. Engr. Bello Muhammad Kiru, Mai bada shawara na musamman fannin Albarkatun ruwa.
  3. Yusuf Shuaibu Imam (Ogan Boye) da aka sake nadawa matsayin Mai bada shawara na Musamman kan matasa da wasannan.
  4. Sai kuma Dr. Nura Jafar Shanono da aka matsar daga matsayin Mai bada shawara na musamman a fannin Albarkatun ruwan, zuwa babban managan hukumar (WRECA).
  5. haka kuma sanarwa ta bayyana daga likkafar Hon. Baba Abubakar Umar daga mai bada shawara na musamman zuwa babban sakataren hukumar dake lura da makarantu masu zaman kansu na jihar kano.
  6. An kuma nada Hon. Nasir Mansur Muhammad a matsayin babban daraktan dake lura da kanana da matsakaitan sana’oi (SMEs)
  7. Aminu Hamidu Bako Kofar Na’isa zai zama mataimakin babbana daraktan (DMD), a ma’aikatar aikin gona da cigaban karkara ta (KNARDA).

haka kuma an nada Engr. Mukhtar Yusuf, matsayin mataimakin babban daraktan (DMD) a hukumar (WRECA).

Daga bisani sanarwar ta tabbatar da cewa nadin ya fara aiki nan take, tare da fatan kammalawa lafiya da nasara.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp