Home Labarai Gwamnan Kano ya sake nada Oga Boye a mukami

Gwamnan Kano ya sake nada Oga Boye a mukami

Gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sake yin sabbin nade-nade a cikin kunshin gwamnatin jihar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan yada labaran gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa.

Sanarwar ta ayyana Farfesa Ibrahim Magaji barde matsayin mai bada shawara na musamman ga mai girma gwamna fannin harajin cikin gida.

  1. Dr. Abdulhamid Danladi, mai bawa Gwamnan shawara kan ‘yan kano mazauna ketare na II
  2. Engr. Bello Muhammad Kiru, Mai bada shawara na musamman fannin Albarkatun ruwa.
  3. Yusuf Shuaibu Imam (Ogan Boye) da aka sake nadawa matsayin Mai bada shawara na Musamman kan matasa da wasannan.
  4. Sai kuma Dr. Nura Jafar Shanono da aka matsar daga matsayin Mai bada shawara na musamman a fannin Albarkatun ruwan, zuwa babban managan hukumar (WRECA).
  5. haka kuma sanarwa ta bayyana daga likkafar Hon. Baba Abubakar Umar daga mai bada shawara na musamman zuwa babban sakataren hukumar dake lura da makarantu masu zaman kansu na jihar kano.
  6. An kuma nada Hon. Nasir Mansur Muhammad a matsayin babban daraktan dake lura da kanana da matsakaitan sana’oi (SMEs)
  7. Aminu Hamidu Bako Kofar Na’isa zai zama mataimakin babbana daraktan (DMD), a ma’aikatar aikin gona da cigaban karkara ta (KNARDA).

haka kuma an nada Engr. Mukhtar Yusuf, matsayin mataimakin babban daraktan (DMD) a hukumar (WRECA).

Daga bisani sanarwar ta tabbatar da cewa nadin ya fara aiki nan take, tare da fatan kammalawa lafiya da nasara.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp