Home Labarai Majalisar Dattijai Ta Tabbatar da Farfesa Abdullahi Saleh A Matsayin Shugaban Hukumar...

Majalisar Dattijai Ta Tabbatar da Farfesa Abdullahi Saleh A Matsayin Shugaban Hukumar NAHCON

Majalisar kasa ta tabbatar da nadin Farfesa Saleh Abdullahi Usman a matsayin sabon shugaban hukumar alhazai ta kasa (NAHCON).

ya karbi mukamin shugaban hukuma na 6 bayan da shugaban kasa Bola Tinubu ya dakatar da tsohon shugabanta Malam Jalal Ahmed Arabi daga shugancin hukumar.

A sanarwar da Mataimakiyar Daraktar harkokin hulda da Jama’a ta Hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, tace, tabbatar da hakan na zuwa ne bayan kwamitin majalisar dattawa kan harkokin kasashen waje ya tantance Farfesa Usman a ranar 8 ga Oktoba 2024.

Tabbatar da hakan ya nuna amincewar Majalisar ga sabon Shugaban Hukumar NAHCON ta hanyar gudanar da ayyukanta na tabbatar da aikin Hajji mai inganci da nasara ga Alhazan Najeriya.

Farfesa Sale Abdullahi ya nuna jin dadinsa kan amanar da bangarorin gwamnati da na majalisar dokoki suka ba shi.

Ya yi alkawarin dorawa kan nasarorin da Shugabanmin da suka gabace shi suka samu wajen tabbatar da ci gaban aikin Hajji a Najeriya, tare da mai da hankali kan jin dadin alhazan Najeriya da yadda za su iya gudanar da aikin Hajji mabrur (Hajji karbabbe).

Bayan Da majalissar dokokin kasar ta tabbatar da Farfesa Usman, ya ba da tabbacin ci gaba da jajircewa wajen ganin hukumar NAHCON ta bunkasa da kuma neman addu’a da goyon bayan kowa wajen cimma burin masu ruwa da tsaki.

“Za mu ci gaba da inganta ayyukanmu ga mahajjatan Najeriya, tare da yin aiki kafada da kafada da duk masu ruwa da tsaki don samar da aikin hajji mai cike da aminci.”

Shugaban ya taba yin aikin a karkashin Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano a matsayin Shugaban Hukumar.

Canjin shugabancin ya zo ne a daidai lokacin da hukumar NAHCON ke shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin bana a daidai lokacin da Saudiyya ta kayyade.

Ana sa ran tabbatar da Shugabancin zai hanzarta shirye-shiryen. Ana kuma sa ran za a kara inganta hadin gwiwar Hukumar da duk masu ruwa da tsaki domin tabbatar da nasarar aikin Hajji ga dukkan maniyyatan Najeriya.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp