Home Labarai Ƴan wasan Super Eagles sun sauka a Kano

Ƴan wasan Super Eagles sun sauka a Kano

Ƴan wasan tawagar Super Eagles ta Najeriya sun koma gida Najeriya, inda suka sauka a filin jirgin Malam Aminu Kano da ke jihar Kano.

Wannan ya biyo bayan tirka-tirka da aka samu bayan ƴan wasan sun isa Libya domin fafatawa da abokan karawarsu na ƙasar Libya, duk da cewa hukumar ƙwallon ƙafar ƙasar ta Libya ta ce ba ta da hannu a lamarin.

Najeriya ta je Libya ne domin fafata wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin Afirka ta 2025, inda aka samu tsaiko, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce musamman a kafofin sadarwa, inda a ƙarshe hukumomi a Najeriya suka buƙaci ƴanwasan su koma gida, sannan ita ma CAF ta ce ta ƙaddamar da bincike a kan lamarin.

Yanzu da ƴan wasan na Najeriya sun sauka a Kano, kamar yadda shafin intanet na tashar talabijin NTA, mallakin gwamnatin Najeriya ya ruwaito.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp