Home AFIRKA Cutar ƙyandar biri ta ɓulla Zimbabwe

Cutar ƙyandar biri ta ɓulla Zimbabwe

Ministan lafiya a ƙasar Zimbabwe ya sanar da ɓullar cutar ƙyandar biri karon farko a ƙasar.

Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun ruwaito cewa waɗanda aka samu da cutar sun haɗa da wani yaro mai shekara 11, da wni matashi mai shekara 24, waɗanda suka yi tafiya daga Afirka ta Kudu da Tanzania a cikin watannin Agusta da Satumba.

Sanarwar da ma’aikatar lafiyar ƙasar ta fitar ta ce: ”Yanzu haka an keɓe dukkan mutanen biyu kuma suna samun kula yadda ya kamata”

Sai dai ma’aikatar lafiyar ta ce ”abubuwa sun lafa” domin haka suke kira ga jama’ar gari ”kada su razana.”

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ayyana dokar ta-ɓaci kan yaƙi da ƙyandar biri ne bayan cutar ta yaɗu daga Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo zuwa ƙasashe masu maƙotaka da ita.

Ita ma cibiyar yaƙi da yaɗuwar cutuka ta Afirka ta ayyana dokar ta-ɓaci a kan cutar, wadda ta ce tana barazana ga al’ummar nahiyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp