Home AFIRKA Cutar ƙyandar biri ta ɓulla Zimbabwe

Cutar ƙyandar biri ta ɓulla Zimbabwe

Ministan lafiya a ƙasar Zimbabwe ya sanar da ɓullar cutar ƙyandar biri karon farko a ƙasar.

Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun ruwaito cewa waɗanda aka samu da cutar sun haɗa da wani yaro mai shekara 11, da wni matashi mai shekara 24, waɗanda suka yi tafiya daga Afirka ta Kudu da Tanzania a cikin watannin Agusta da Satumba.

Sanarwar da ma’aikatar lafiyar ƙasar ta fitar ta ce: ”Yanzu haka an keɓe dukkan mutanen biyu kuma suna samun kula yadda ya kamata”

Sai dai ma’aikatar lafiyar ta ce ”abubuwa sun lafa” domin haka suke kira ga jama’ar gari ”kada su razana.”

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ayyana dokar ta-ɓaci kan yaƙi da ƙyandar biri ne bayan cutar ta yaɗu daga Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo zuwa ƙasashe masu maƙotaka da ita.

Ita ma cibiyar yaƙi da yaɗuwar cutuka ta Afirka ta ayyana dokar ta-ɓaci a kan cutar, wadda ta ce tana barazana ga al’ummar nahiyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp