Home AFIRKA Cutar ƙyandar biri ta ɓulla Zimbabwe

Cutar ƙyandar biri ta ɓulla Zimbabwe

Ministan lafiya a ƙasar Zimbabwe ya sanar da ɓullar cutar ƙyandar biri karon farko a ƙasar.

Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun ruwaito cewa waɗanda aka samu da cutar sun haɗa da wani yaro mai shekara 11, da wni matashi mai shekara 24, waɗanda suka yi tafiya daga Afirka ta Kudu da Tanzania a cikin watannin Agusta da Satumba.

Sanarwar da ma’aikatar lafiyar ƙasar ta fitar ta ce: ”Yanzu haka an keɓe dukkan mutanen biyu kuma suna samun kula yadda ya kamata”

Sai dai ma’aikatar lafiyar ta ce ”abubuwa sun lafa” domin haka suke kira ga jama’ar gari ”kada su razana.”

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ayyana dokar ta-ɓaci kan yaƙi da ƙyandar biri ne bayan cutar ta yaɗu daga Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo zuwa ƙasashe masu maƙotaka da ita.

Ita ma cibiyar yaƙi da yaɗuwar cutuka ta Afirka ta ayyana dokar ta-ɓaci a kan cutar, wadda ta ce tana barazana ga al’ummar nahiyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp