Home Labarai APC ta gargaɗi Ndume kan sukar gwamnatin Tinubu

APC ta gargaɗi Ndume kan sukar gwamnatin Tinubu

Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta shawarci tsohon mai tsawatarwa na majalisar dattawan ƙasar, Sanata Ali Ndume kan ya riƙa gabatar da ƙorafin sa kai tsaye ga shugaba Bola Tinubu, a madadin fita fili yana sukar tsare-tsaren gwamnati.

Daraktan yaɗa labaran jam’iyyar APC na ƙasa, Bala Ibrahim ne ya bayyana hakan ga manema labarai inda ya ce kowanne ɗan ƙasa yana da ƴancin bayyana ra’ayin sa a tsarin dimokuraɗiyya, amma akwai buƙatar manyan ƴan siyasa irin su Ndume su riƙa kiyaye irin bayanan da zasu yi a bainar jama’a.

Sanata Ndume mai wakiltar mazaɓar Borno ta Kudu a majalisar dattawan Najeriya ya bayyana a cikin shirin Ra’ayi Riga na BBC Hausa, inda ya buƙaci gwamnatin shugaba Tinubu ta ɗauki matakan kawo sauƙin halin matsi da ƴan Najeriya ke ciki, ya yi kiran a dakatar da ƙarin farashin mai a ƙasar.

Sanata Ndume ya kuma fitar da wata sanarwa ga manema labarai domin jaddada matsayar sa a kan halin da ake ciki, inda ya yi iƙirarin cewa akwai wasu da ke tunzura gwamnati tana aiwatar da tsare-tsare masu tsauri.

A watannin baya ma jam’iyyar APC ta nemi majalisar dattawa ta ladabtar da Sanata Ndume ta hanyar ƙwace mukamin sa na mai tsawatarwa saboda yadda ya ke fita kafafen yaɗa labarai yana sukar gwamnatin APC.

Daga baya sanatan ya nemi afuwa kuma jam’iyyar ta yafe masa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp