Home Labarai Tinubu ya yi tir da yadda aka ci zarafin tawagar Super Eagles...

Tinubu ya yi tir da yadda aka ci zarafin tawagar Super Eagles a Libya

Shugaba Bola Tinubu ya yi tir da yadda aka ci zarafin tawagar Super Eagles ta Najeriya a filin jirgin sama na kasar Libya, yana mai kira ga Hukumar Kwallon Kafa ta Afrika (CAF) da ta gudanar da cikakken bincike a kai.

Rahotanni sun nuna cewa an sanya ƴan wasan cikin mawuyacin hali, lamarin da ya tilasta musu janyewa daga wasan da aka shirya yi a ranar Talata, kamar yanda Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya (NFF) ta tabbatar.

A wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai da tsare-tsare, Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya bukaci Kwamitin Ladabtarwa na CAF da ya binciki wannan al’amari tare da hukunta wadanda suka karya dokokin CAF.

Ya jaddada cewa matakan da za a dauka ya zama darasi domin hana sake faruwar irin wannan lamari a nan gaba.

Da yake magana kan yanda aka dauki mataki cikin hanzari, Shugaban ya yaba wa Ma’aikatar Harkokin Kasashen Waje da Ma’aikatar Bunƙasa Wasanni ta Tarayya bisa hadin gwiwar da suka yi, wanda ya tabbatar da dawowar tawagar Super Eagles lafiya.

Wannan ba shi ne karo na farko da aka fuskanci matsala kan tawagogin kwallon kafa na Najeriya a kasashen waje ba.

A shekarar 2019, Super Falcons sun sha irin wannan cin zarafi a kasar Aljeriya, wanda ya sa aka fara tashin hankali kan yanda ake mu’amala da tawagogin kwallon kafa na Afrika a wasannin kasa da kasa.

Duk da wannan matsala da aka samu, Shugaba Tinubu ya jinjinawa Super Eagles bisa jarumtar da suka nuna, inda ya bayyana muhimmancin kwallon kafa a matsayin wata hanya ta hadin kai ga kasa.

Ya kuma yi kira ga hukumomin kwallon kafa da masu sha’awar wasan da su haɗa kai wajen tabbatar da adalci da kuma ganin cewa tawagogin suna samun kima da mutunci a duk inda suka je.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp