Home Labarai Tinubu ya yi tir da yadda aka ci zarafin tawagar Super Eagles...

Tinubu ya yi tir da yadda aka ci zarafin tawagar Super Eagles a Libya

Shugaba Bola Tinubu ya yi tir da yadda aka ci zarafin tawagar Super Eagles ta Najeriya a filin jirgin sama na kasar Libya, yana mai kira ga Hukumar Kwallon Kafa ta Afrika (CAF) da ta gudanar da cikakken bincike a kai.

Rahotanni sun nuna cewa an sanya ƴan wasan cikin mawuyacin hali, lamarin da ya tilasta musu janyewa daga wasan da aka shirya yi a ranar Talata, kamar yanda Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya (NFF) ta tabbatar.

A wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai da tsare-tsare, Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya bukaci Kwamitin Ladabtarwa na CAF da ya binciki wannan al’amari tare da hukunta wadanda suka karya dokokin CAF.

Ya jaddada cewa matakan da za a dauka ya zama darasi domin hana sake faruwar irin wannan lamari a nan gaba.

Da yake magana kan yanda aka dauki mataki cikin hanzari, Shugaban ya yaba wa Ma’aikatar Harkokin Kasashen Waje da Ma’aikatar Bunƙasa Wasanni ta Tarayya bisa hadin gwiwar da suka yi, wanda ya tabbatar da dawowar tawagar Super Eagles lafiya.

Wannan ba shi ne karo na farko da aka fuskanci matsala kan tawagogin kwallon kafa na Najeriya a kasashen waje ba.

A shekarar 2019, Super Falcons sun sha irin wannan cin zarafi a kasar Aljeriya, wanda ya sa aka fara tashin hankali kan yanda ake mu’amala da tawagogin kwallon kafa na Afrika a wasannin kasa da kasa.

Duk da wannan matsala da aka samu, Shugaba Tinubu ya jinjinawa Super Eagles bisa jarumtar da suka nuna, inda ya bayyana muhimmancin kwallon kafa a matsayin wata hanya ta hadin kai ga kasa.

Ya kuma yi kira ga hukumomin kwallon kafa da masu sha’awar wasan da su haɗa kai wajen tabbatar da adalci da kuma ganin cewa tawagogin suna samun kima da mutunci a duk inda suka je.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp