Home Labarai Tinubu ya yi tir da yadda aka ci zarafin tawagar Super Eagles...

Tinubu ya yi tir da yadda aka ci zarafin tawagar Super Eagles a Libya

Shugaba Bola Tinubu ya yi tir da yadda aka ci zarafin tawagar Super Eagles ta Najeriya a filin jirgin sama na kasar Libya, yana mai kira ga Hukumar Kwallon Kafa ta Afrika (CAF) da ta gudanar da cikakken bincike a kai.

Rahotanni sun nuna cewa an sanya ƴan wasan cikin mawuyacin hali, lamarin da ya tilasta musu janyewa daga wasan da aka shirya yi a ranar Talata, kamar yanda Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya (NFF) ta tabbatar.

A wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai da tsare-tsare, Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya bukaci Kwamitin Ladabtarwa na CAF da ya binciki wannan al’amari tare da hukunta wadanda suka karya dokokin CAF.

Ya jaddada cewa matakan da za a dauka ya zama darasi domin hana sake faruwar irin wannan lamari a nan gaba.

Da yake magana kan yanda aka dauki mataki cikin hanzari, Shugaban ya yaba wa Ma’aikatar Harkokin Kasashen Waje da Ma’aikatar Bunƙasa Wasanni ta Tarayya bisa hadin gwiwar da suka yi, wanda ya tabbatar da dawowar tawagar Super Eagles lafiya.

Wannan ba shi ne karo na farko da aka fuskanci matsala kan tawagogin kwallon kafa na Najeriya a kasashen waje ba.

A shekarar 2019, Super Falcons sun sha irin wannan cin zarafi a kasar Aljeriya, wanda ya sa aka fara tashin hankali kan yanda ake mu’amala da tawagogin kwallon kafa na Afrika a wasannin kasa da kasa.

Duk da wannan matsala da aka samu, Shugaba Tinubu ya jinjinawa Super Eagles bisa jarumtar da suka nuna, inda ya bayyana muhimmancin kwallon kafa a matsayin wata hanya ta hadin kai ga kasa.

Ya kuma yi kira ga hukumomin kwallon kafa da masu sha’awar wasan da su haɗa kai wajen tabbatar da adalci da kuma ganin cewa tawagogin suna samun kima da mutunci a duk inda suka je.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp