Home Labarai Akwai yiwuwar samun ambaliyar ruwa a a wasu jihohin Nijeriya 22

Akwai yiwuwar samun ambaliyar ruwa a a wasu jihohin Nijeriya 22

Gwamnatin Najeriya ta yi hasashen kwashe kwana biyar ana mamakon ruwa, wanda zai iya jawo ambaliya a jihohi 22 na babban birnin tarayyar ƙasar, inda ta yi gargaɗi ga garuruwan da suke bakin tekunan Donga da Binue da Ogun su tashi daga yankunan.

Jaridar Punch ce ta ruwaito hakan a ranar Litinin daga ma’aikatar muhalli.

Rohoton na kwamitin bayar da gargaɗi na ma’aikatar ya ƙara da cewa za a iya fuskantar ambaliyar ne a ranar 14 da 18 na watan Oktoba.

Jihohin da yankunan da za su iya fuskantar ambaliyar sun haɗa da jihar Osun (Ede, Ile-Ife, Ilesa, Osogbo); jihar Delta (Escravos); jihar Kuros Riba (Ikom); jihar Anambra (Onitsha); jihar Taraba (Donga, Ibi, Wukari, Bandawa, Beli, Bolleri, Dampar, Duchi, Garkowa, Gassol, Gungun Bodel, Kambari, Kwata Kanawa, Lau, Mayo Ranewo, Mutum Biyu, Ngaruwa, Serti, Yorro); jihar Nasarawa (Rukubi); jihar Kebbi (Argungu, Birnin-Kebbi, Gwandu, Kalgo, Ribah, Sakaba, Yelwa); jihar Gombe (Bajoga); jihar Katsina (Bakori, Funtua); jihar Borno (Biu, Briyel); jihar Kaduna (Birnin-Gwari, Buruku, Kaduna, Jaji); jihar Niger (Bida, Kontagora, Lapai, Lavun, Magama, Mashegu, Mokwa, New Bussa, Rijau, Sarkin Pawa, Suleja, Wushishi).

Sauran su ne jihar Yobe (Dapchi); Adamawa (Demsa, Farkumo, Ganye, Gbajili, Jimeta, Mayo-Belwa, Mubi, Natubi, Numan, Song, Shelleng, Wuro Bokki); Kogi (Ibaji, Omala); Kwara (Jebba, Kosubosu); Bauchi (Kari, Tafawa Balewa, Kirfi); Plateau (Shendam); babban birnin tarayya Abuja (Kubwa, Gwagwalada, Bwari); Kano (Sumaila); Oyo (Kishi); Sokoto (Silame); da Zamfara (Majara).

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp