Home Labarai Akwai yiwuwar samun ambaliyar ruwa a a wasu jihohin Nijeriya 22

Akwai yiwuwar samun ambaliyar ruwa a a wasu jihohin Nijeriya 22

Gwamnatin Najeriya ta yi hasashen kwashe kwana biyar ana mamakon ruwa, wanda zai iya jawo ambaliya a jihohi 22 na babban birnin tarayyar ƙasar, inda ta yi gargaɗi ga garuruwan da suke bakin tekunan Donga da Binue da Ogun su tashi daga yankunan.

Jaridar Punch ce ta ruwaito hakan a ranar Litinin daga ma’aikatar muhalli.

Rohoton na kwamitin bayar da gargaɗi na ma’aikatar ya ƙara da cewa za a iya fuskantar ambaliyar ne a ranar 14 da 18 na watan Oktoba.

Jihohin da yankunan da za su iya fuskantar ambaliyar sun haɗa da jihar Osun (Ede, Ile-Ife, Ilesa, Osogbo); jihar Delta (Escravos); jihar Kuros Riba (Ikom); jihar Anambra (Onitsha); jihar Taraba (Donga, Ibi, Wukari, Bandawa, Beli, Bolleri, Dampar, Duchi, Garkowa, Gassol, Gungun Bodel, Kambari, Kwata Kanawa, Lau, Mayo Ranewo, Mutum Biyu, Ngaruwa, Serti, Yorro); jihar Nasarawa (Rukubi); jihar Kebbi (Argungu, Birnin-Kebbi, Gwandu, Kalgo, Ribah, Sakaba, Yelwa); jihar Gombe (Bajoga); jihar Katsina (Bakori, Funtua); jihar Borno (Biu, Briyel); jihar Kaduna (Birnin-Gwari, Buruku, Kaduna, Jaji); jihar Niger (Bida, Kontagora, Lapai, Lavun, Magama, Mashegu, Mokwa, New Bussa, Rijau, Sarkin Pawa, Suleja, Wushishi).

Sauran su ne jihar Yobe (Dapchi); Adamawa (Demsa, Farkumo, Ganye, Gbajili, Jimeta, Mayo-Belwa, Mubi, Natubi, Numan, Song, Shelleng, Wuro Bokki); Kogi (Ibaji, Omala); Kwara (Jebba, Kosubosu); Bauchi (Kari, Tafawa Balewa, Kirfi); Plateau (Shendam); babban birnin tarayya Abuja (Kubwa, Gwagwalada, Bwari); Kano (Sumaila); Oyo (Kishi); Sokoto (Silame); da Zamfara (Majara).

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp