Home General Ƴan bindiga sun harbi babban kwamandan dakarun sa kai na jihar Zamfara

Ƴan bindiga sun harbi babban kwamandan dakarun sa kai na jihar Zamfara

'Yan Ta'adda

A Wata musayar wuta da aka yi a tsakanin ƴan bindiga da dakarun tsaro na sakai CPG a jihar Zamfara dake Arewacin Najeriya, ƴan ta’addar sun kashe mutane dama inda suka raunata wasu cki har da babban kwamandan rundunar ƴan sa kan Janar Lawal B. Muhammad mai ritaya.

Rahotanni dai sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun tare hanyar Funtua zuwa Tsafe ne mai cike da cunkoson jama’a da yammacin ranar lahadi, inda suka far wa masu ababen hawa ciki har da Darakta janar na hukumar ta CPG.

Sannan a yayin wannan samamen ƴan bindigar sun yi  awun gaba da wasu fasinjoji da dama dake kan hanyarsu ta zuwa wurare daban-daban.

Wata majiya daga ma’aikatar tsaron cikin gida ta jihar Zamfara, wadda ta bukaci a sakaya sunanta, ta tabbatar da faruwar lamarin, ta kuma ce shugaban na samun kulawa a wani asibiti da ke Gusau, babban birnin jihar.

Wannan arin na zuwa ne kwanaki kadan bayan da ‘yan bindiga suka kashe jami’an na CPG akalla takwas da wani direban motar  sufuri a karamar hukumar Tsafe da ke jihar ta Zamfara.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi wa jami’an na CPG kwanton bauna ne kafin su an kara suka bude musu wuta.

Da yake bayani game da harin, babban kwamandan da aka harba ya bayyana cewa, bayan da ya fahimci cewa ‘yan bindigar na shirin kai hari a tsafe, sai ya tura jami’an CPG 105 zuwa karamar hukumar tare da ajiye su a wannan wuri domin baiwa matafiya kariya ba tare da sanin sun musu riga Malam masallaci ba.

Sai gashi abin bakin ciki ƴan bindigar sukai musu kwanton bauna saboda sun kwana a wurin, a yayin da dakarun sa kan suke sauka sai suka bude musu wuta kuma suka kashe wasu daga cikinsu tare da jikkata wasu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga Legas
X whatsapp