Home AFIRKA Faye ya ƙaddamar da shiri mai dogon zango dan ciyar da Senegal...

Faye ya ƙaddamar da shiri mai dogon zango dan ciyar da Senegal gaba

Gwamnatin Senegal ta ƙaddamar da shirinta mai nisan zango na ciyar da ƙasar gaba, wanda take fatan za a kammala aiwatar da shi cikin shekaru 25 masu zuwa.

Sai dai gwamnatin Senegal ɗin ta bayyana wasu daga cikin muradun da tsara cim-musu cikin shekaru 5.

Muhimman muradun da take fatan cim-musu a gejeren zango kuwa, sun haɗa da rage nauyin bashin da ke kan ƙasar daga kaso 83.7 zuwa kaso 70 cikin 100.

Sai kuma rage giɓin kasafin kuɗi zuwa kashi 3 nan gaba kaɗan, saɓanin giɓin kashi 10.4 da ƙididdiga ta nuna cewar gwa,natin senegal din ta yi fama da shi daga shekarar 2019 zuwa 2023.

Ƙalubale na gaba da gwamnatin Senegal ta sha alwashin magancewa shi ne matsin rayuwa, inda ta yi alƙawarin cikin shekaru biyar da ke tafe, za ta ƙara yawan matsakaicin albashin da ‘yan ƙasar ke samu da kashi 50 cikin 100, kwatankwacin ƙarin daga dala dubu 1, 660 zuwa aƙalla dala dubu 2,648, yayin da kuma za a rage hauhawar farashin kayayyaki zuwa kashi 2 cikin shekaru 5.

Shugaban Senegal Basirou Diomaye Faye da Fira Ministansa Ousmane Sonko ne suka jagoranci kaddamar da gagarumin shirin a garin Diamniadio, mai nisan kilomita 30 daga Dakar babban birnin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp