Home General Gwamnatin Kano ta zargi alkali Amobeda

Gwamnatin Kano ta zargi alkali Amobeda

Gwamnatin Jihar Kano ta zargi Mai shari’a Simon Amobeda na Babbar Kotun Tarayya da nuna son zuciya a shari’ar zaben kananan hukumomi da aka gabatar gabansa.

Jam’iyyar APC ce dai tare da wasu masu ruwa da tsaki su ka shigar da kara su na neman kotu ta bayyana cewa ba a samu zababbun shugabannin kananan hukumomi ba a jihar Kano.

Jaridar GUARDIAN ta rawaito cewa a zaman fara sauraren korafe-korafen da aka shigar a jiya Juma’a, Antoni Janar na Jihar Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Isa Haruna Dederi, ya nemi Mai Shari’a Amobeda ya janye kansa daga shari’ar saboda zargin nuna son zuciya da ya ce alkalin ya yi a lokuta da dama a kan gwamnatin Kano.

A cikin takardar da ya gabatar, Dederi ya yi zargin cewa mai shari’ar yana da wata kiyaiya a zuciyar shi da ya nuna ga gwamnatin jihar da hukumominta tun bayan da aka shigar da wani korafi ga Hukumar Kula da Alkalai ta Kasa (NJC) da ke zarginsa da cin gajiyar iko da kuma bayar da umarni ba bisa ka’ida ba.

Gwamnatin jihar ta bayyana cewa ta lura da “wadansu abubuwan da ba su dace ba” musamman game da shari’o’in da suka shafi mutanen da ke da alaka da siyasa, musamman wadanda ke cikin jam’iyyun adawa, da aka gabatar gabansa. Wannan, a cewar gwamnatin, yana nuna wata alaka tsakanin mai shari’ar da wata jam’iyyar adawa.

Gwamnati ta kuma ce “Mai shari’ar ya sha fitowa a jaridu yana barazanar fallasa wani jami’in gwamnatin Jihar Kano da ya rubuta karar a kansa, yana nuna fushinsa tare da kokarin tabbatar da cewa karar ba ta dace ba.”

Duk da haka, Mai shari’a Amobeda, yayin nuna rashin amincewa da bukatar da gwamnatin ta gabatar na ya janye kansa daga shari’ar, ya ce ba ya goyon bayan wani bangare kamar yadda ake zarginsa, sai dai yana goyon bayan adalci ne kawai.

Mai shari’ar, yana martani, ya ce, “Lauyoyi marasa kwazo ne kawai ke gabatar da bukatar alkali ya janye kansa daga shari’a,” sannan ya zargi lauyoyin Jihar Kano da yin “abubuwa marasa kyau” a kansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp