Home General Kashi biyu cikin uku na gidajen Najeriya ba su samun lafiyayyen abinci...

Kashi biyu cikin uku na gidajen Najeriya ba su samun lafiyayyen abinci – NBS

Wani bincike da Hukumar ƙididdiga ta Najeriya NBS ta gudanar ya gano cewa rashin wadata ya sa kashi biyu cikin uku na gidaje a Najeriya ba su iya samun lafiyayyen abinci mai ɗauke da ingantattun sinadarai.

Binciken da hukumar ta gudanar ya mayar da hankali ne kan ƙaruwar talauci a tsakanin gidajen ƙasar da irin tasirin da hakan ke yi wajen raguwar sayen abubuwa da ‘yan ƙasar suka yi sakamakon tashin farashinsu.

“Kusan kashi biyu cikin uku na gidajen Najeriya ba su iya cin lafiyayyen abinci mai ɗauke da sinadarai ko su dafa abinci saboda rashin wadata da suke fama da shi”, kamar yadda rahoton binciken ya nuna.

Haka kuma binciken ya gano cewa kashi 63.8 cikin 100 na gidajen ƙasar na cin abincin ɗan kaɗan saboda rashin kuɗi, yayin da kashi 62.4 na gidajen ke cikin fargabar rashin samun wadataccen abinci, sannan kuma kashi 60.5 cikin 100 na gidajen ba sa iya cin abincin da ya kamata a ce suna ci.

Rahoton binciken na zuwa ne ƙasa da wata guda bayan da wani rahoto da gwamnatin Najeriya ta fitar tare da tallafin Majalisar Dinkin Duniya ya nuna cewa ‘yan ƙasar fiye da miliyan 33 za su fuskanci matsalar ƙarancin abinci a 2025.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp