Home General Kashi biyu cikin uku na gidajen Najeriya ba su samun lafiyayyen abinci...

Kashi biyu cikin uku na gidajen Najeriya ba su samun lafiyayyen abinci – NBS

Wani bincike da Hukumar ƙididdiga ta Najeriya NBS ta gudanar ya gano cewa rashin wadata ya sa kashi biyu cikin uku na gidaje a Najeriya ba su iya samun lafiyayyen abinci mai ɗauke da ingantattun sinadarai.

Binciken da hukumar ta gudanar ya mayar da hankali ne kan ƙaruwar talauci a tsakanin gidajen ƙasar da irin tasirin da hakan ke yi wajen raguwar sayen abubuwa da ‘yan ƙasar suka yi sakamakon tashin farashinsu.

“Kusan kashi biyu cikin uku na gidajen Najeriya ba su iya cin lafiyayyen abinci mai ɗauke da sinadarai ko su dafa abinci saboda rashin wadata da suke fama da shi”, kamar yadda rahoton binciken ya nuna.

Haka kuma binciken ya gano cewa kashi 63.8 cikin 100 na gidajen ƙasar na cin abincin ɗan kaɗan saboda rashin kuɗi, yayin da kashi 62.4 na gidajen ke cikin fargabar rashin samun wadataccen abinci, sannan kuma kashi 60.5 cikin 100 na gidajen ba sa iya cin abincin da ya kamata a ce suna ci.

Rahoton binciken na zuwa ne ƙasa da wata guda bayan da wani rahoto da gwamnatin Najeriya ta fitar tare da tallafin Majalisar Dinkin Duniya ya nuna cewa ‘yan ƙasar fiye da miliyan 33 za su fuskanci matsalar ƙarancin abinci a 2025.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp