Home General Atiku ya gargaɗi Tinubu kan yawan ciyo bashi

Atiku ya gargaɗi Tinubu kan yawan ciyo bashi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar ya ce yawaitar ciyo basussuka da gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu ke yi zai ƙara jefa tattalin arzikin Najeriya cikin ƙunci.

Atiku ya bayyana haka ne a wani rubuta da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya ce, “rahoton da bankin duniya ya fitar kwanan nan, wanda ke nuna cewa Najeriya ce ƙasa ta uku da ta fi cin bashi daga hukumomin kuɗi na duniya abin damuwa ne.

Tsohon ɗantakarar na PDP ya kuma soki yadda majalisar dokoki ke amincewa da buƙatar ciyo basussukan, waɗanda a cewarsa suke ƙara jefa ƙasar cikin ƙangin bashi.

“Rahoton ya fito ne a daidai lokacin da gwamnatin ƙasar ta aike da wani buƙatar sake ciyo wani bashin na naira triliyan 1.7 saboda cike giɓin kasafin kuɗin 2024. Abin da zai ƙara ɗaga hankali a game da bashin ma shi ne kasancewarar a kasafin kuɗin, an kasafta darajar dala ɗaya a kan naira 800, alhali yanzu dala ta kai naira 1,600.”

Ya ƙara da cewa Najeriya na ƙara nutsewa a cikin bashi, “sannan majalisar dokoki suna taimakawa. Tinubu ya bayyana a watan Yuli cewa hukumar tattara haraji da kwastam sun tara kuɗin shiga da ba a taɓa tarawa ba. To me ya sa ake cin bashin? akwai wani abu da suke ɓoyewa ƴan Najeriya.”

Atiku ya ƙara da cewa yawan cin bashin yana ƙara takurawa tattalin arzikin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp