Home General Sojoji sun fatattaki Lakurawa daga Najeriya – Sanata Aliero

Sojoji sun fatattaki Lakurawa daga Najeriya – Sanata Aliero

Sanata mai wakiltar Kebbi ta tsakiya, Adamu Aliero, ya ce sojojin Najeriya sun samu nasarar fatattakar ƴan Lakurawa, inda suka tsallaka zuwa Nijar.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, Aliero ya ce an samu nasarar ne bayan ɗaukar matakin da ministan tsaro Abubakar Bagudu da babban hafsan tsaro da sauran masu ruwa da tsaki suka ɗauka, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Aliero ya ce, “mun faɗa wa ministan cewa idan aka yi sakaci da ƴan ta’addan Lakurawa, za a iya maimaita abin da ya faru a arewa maso gabas a arewa maso yamma. Yaƙi ne da za a iya gamawa a kwana biyar, amma idan aka yi sakaci, lamarin zai ƙazance saboda yankin arewa maso yamma ya fi yawan mutane kuma ya fi arziki da ma girman ƙasar noma da kiwo.

“Amma kun san da sojoji suka zo a ranar Talata (12 ga Nuwamba) sun samu nasarar fatattakarsu zuwa Jamhuriyar Nijar?”

Ƴan Lakurawa sun kashe mutane da dama a jihar Kebbi, lamarin da ya sa Sanata Aliero da sauran ƴan majalisar jihar suka kai ziyara a ƙananan hukumomin Argungu da Augie domin gane wa idonsu irin ɓarnar da suke yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp