Home General Sojoji sun fatattaki Lakurawa daga Najeriya – Sanata Aliero

Sojoji sun fatattaki Lakurawa daga Najeriya – Sanata Aliero

Sanata mai wakiltar Kebbi ta tsakiya, Adamu Aliero, ya ce sojojin Najeriya sun samu nasarar fatattakar ƴan Lakurawa, inda suka tsallaka zuwa Nijar.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, Aliero ya ce an samu nasarar ne bayan ɗaukar matakin da ministan tsaro Abubakar Bagudu da babban hafsan tsaro da sauran masu ruwa da tsaki suka ɗauka, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Aliero ya ce, “mun faɗa wa ministan cewa idan aka yi sakaci da ƴan ta’addan Lakurawa, za a iya maimaita abin da ya faru a arewa maso gabas a arewa maso yamma. Yaƙi ne da za a iya gamawa a kwana biyar, amma idan aka yi sakaci, lamarin zai ƙazance saboda yankin arewa maso yamma ya fi yawan mutane kuma ya fi arziki da ma girman ƙasar noma da kiwo.

“Amma kun san da sojoji suka zo a ranar Talata (12 ga Nuwamba) sun samu nasarar fatattakarsu zuwa Jamhuriyar Nijar?”

Ƴan Lakurawa sun kashe mutane da dama a jihar Kebbi, lamarin da ya sa Sanata Aliero da sauran ƴan majalisar jihar suka kai ziyara a ƙananan hukumomin Argungu da Augie domin gane wa idonsu irin ɓarnar da suke yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp