Home General Matakan bunƙasa tattalin arzikin ka na matuƙar illa ga talakawan Arewa –...

Matakan bunƙasa tattalin arzikin ka na matuƙar illa ga talakawan Arewa – ACF

Ƙungiyar kare martabar ƴan Arewacin Najeriya ta ACF, ta buƙaci shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta sake fasalin matakan da yake ɗauka domin bunkasa tattalin arzikin ƙasar, saboda abinda suka kira matuƙar illar da yake yiwa talakawan da ke yankin.

Bayan wani taro da ta gudanar, wanda ya yi nazari a kan irin manufofi da matakan da gwamnatin ke ɗauka, ƙungiyar ta ce rayuwar talakawan Najeriya na kara tabarbarewa musamman mazauna yankin arewacin ƙasar da ke fuskantar ƙalubale daban daban.

Sanarwar da mai magana da yawun ƙungiyar Farfesa Tukur Muhammad-Baba ya rabawa manema labarai, ta ce mazauna yankin arewacin ƙasar na fama da tsananin rashin abinci da tsaro da ƙarancin samun damar ilimi da koyan sana’o’i da kuma harkokin kasuwancin da za su dogara da kansu.

Muhammad-Baba ya ce rayuwar akasarin mutanen arewacin ƙasar ya dogara ne ga ƙananan sana’oi, amma yanayin da ake ciki ya jefa da dama daga cikin su cikin halin ƙaƙanikayi da kuma rashin madogara, sakamakon manufofin tattalin arzikin da wannan gwamnatin ke ɗauka a matakin tarayya, ba tare da la’akari da irin uƙubar da yake jefa jama’a ba.

Ƙungiyar ta ce duk da yake ɗaukar irin waɗannan matakai na da matukar tasiri, amma kuma bai da ce ya yi illa ga mutanen da ake cewa ana yi domin su ba, saboda yanayin da ake ciki na iya hallaka wasu daga cikin su ta hanyar da ba za su iya cin moriyar gajiyar da za’a samu ba.

Muhammad-Baba ya ce sun buƙaci shugaban ƙasar da ya sake nazarin takunsa ta hanyar da zai dinga la’akari da rayuwar jama’a, tare da kuma sauraron ƙorafin jama’a domin gyara ga matakan da suke ɗauka waɗanda ke yiwa ƴan ƙasa illa.

ACF ta buƙaci ɗaukar matakan gaggawa ta hanyar aiwatar da manufofin kar-ta-kwana da kuma na dogon zango ta hanyar da za’a samarwa jama’a abinci, ciki hara da shigo da shi daga ƙasashen ƙetare, domin ragewa jama’a raɗaɗin halin da suke ciki.

Ƙungiyar wadda ta ce ta fahimci ƴan arewa ne kawai za su kare martabar yankin, ta buƙaci samun daidaito wajen raba mukamai da kuma gaggauta samo maslaha dangane da matsalar samar da wutar lantarki da talaucin da ya addabi jama’a da rashin ayyukan yi da kuma koma bayan da yankin ke fuskanta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a Jihar
X whatsapp