Home General Matakan bunƙasa tattalin arzikin ka na matuƙar illa ga talakawan Arewa –...

Matakan bunƙasa tattalin arzikin ka na matuƙar illa ga talakawan Arewa – ACF

Ƙungiyar kare martabar ƴan Arewacin Najeriya ta ACF, ta buƙaci shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta sake fasalin matakan da yake ɗauka domin bunkasa tattalin arzikin ƙasar, saboda abinda suka kira matuƙar illar da yake yiwa talakawan da ke yankin.

Bayan wani taro da ta gudanar, wanda ya yi nazari a kan irin manufofi da matakan da gwamnatin ke ɗauka, ƙungiyar ta ce rayuwar talakawan Najeriya na kara tabarbarewa musamman mazauna yankin arewacin ƙasar da ke fuskantar ƙalubale daban daban.

Sanarwar da mai magana da yawun ƙungiyar Farfesa Tukur Muhammad-Baba ya rabawa manema labarai, ta ce mazauna yankin arewacin ƙasar na fama da tsananin rashin abinci da tsaro da ƙarancin samun damar ilimi da koyan sana’o’i da kuma harkokin kasuwancin da za su dogara da kansu.

Muhammad-Baba ya ce rayuwar akasarin mutanen arewacin ƙasar ya dogara ne ga ƙananan sana’oi, amma yanayin da ake ciki ya jefa da dama daga cikin su cikin halin ƙaƙanikayi da kuma rashin madogara, sakamakon manufofin tattalin arzikin da wannan gwamnatin ke ɗauka a matakin tarayya, ba tare da la’akari da irin uƙubar da yake jefa jama’a ba.

Ƙungiyar ta ce duk da yake ɗaukar irin waɗannan matakai na da matukar tasiri, amma kuma bai da ce ya yi illa ga mutanen da ake cewa ana yi domin su ba, saboda yanayin da ake ciki na iya hallaka wasu daga cikin su ta hanyar da ba za su iya cin moriyar gajiyar da za’a samu ba.

Muhammad-Baba ya ce sun buƙaci shugaban ƙasar da ya sake nazarin takunsa ta hanyar da zai dinga la’akari da rayuwar jama’a, tare da kuma sauraron ƙorafin jama’a domin gyara ga matakan da suke ɗauka waɗanda ke yiwa ƴan ƙasa illa.

ACF ta buƙaci ɗaukar matakan gaggawa ta hanyar aiwatar da manufofin kar-ta-kwana da kuma na dogon zango ta hanyar da za’a samarwa jama’a abinci, ciki hara da shigo da shi daga ƙasashen ƙetare, domin ragewa jama’a raɗaɗin halin da suke ciki.

Ƙungiyar wadda ta ce ta fahimci ƴan arewa ne kawai za su kare martabar yankin, ta buƙaci samun daidaito wajen raba mukamai da kuma gaggauta samo maslaha dangane da matsalar samar da wutar lantarki da talaucin da ya addabi jama’a da rashin ayyukan yi da kuma koma bayan da yankin ke fuskanta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp