Home General Yanzu-yanzu: Majalisar Wakilai ta ki amincewa da kudirin neman karawa shugaban kasa...

Yanzu-yanzu: Majalisar Wakilai ta ki amincewa da kudirin neman karawa shugaban kasa wa’adi

Majalisar wakilai ta yi watsi da kudirin dokar da ke neman mayar da wa’adin shugabancin Najeriya ya koma shekaru shida, amma falle daya.

An yi watsi da kudirin dokar, wanda ake shirin yiwa karatu na biyu a yayin zaman taron na ranar Alhamis.

Kudirin dokar dai da ya wuce zai sauya tanade-tanaden kundin tsarin mulkin Nigeriya, na samar da wa’adin mulki na shekaru shida ga shugaban kasa da gwamnonin jihohi.

Hon. Ikenga Ugochinyere ne ya gabatar da kudirin , Wanda ya bukaci wa’adin mulkin Shugaban kasa da gwamnoni da shugabannin kananan hukumomi ya koma falle daya amma ya kai shekaru shida .

Kudirin ya kuma nemi a ba da damar gudanar da dukkan zabukan shugaban kasa, gwamna da yan majalisu duk a rana daya.

A lokacin da aka kada kuri’a a kan kudirin dokar da aka shirya yi wa karatu na biyu, yawancin ‘yan majalisar sun kada kuri’ar kin amincewa da shi.

Idan za a iya tunawa a kwanakin baya tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya bayar da shawarar a gyara kundin tsarin mulkin kasar na 1999 da dokar zabe ta 2022, saboda a bada dama wa’adin shugaban kasa ya koma na tsawon shekaru shida, sannan a rika baiwa kowacce shiyya dama.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp