Home General Yanzu-yanzu: Majalisar Wakilai ta ki amincewa da kudirin neman karawa shugaban kasa...

Yanzu-yanzu: Majalisar Wakilai ta ki amincewa da kudirin neman karawa shugaban kasa wa’adi

Majalisar wakilai ta yi watsi da kudirin dokar da ke neman mayar da wa’adin shugabancin Najeriya ya koma shekaru shida, amma falle daya.

An yi watsi da kudirin dokar, wanda ake shirin yiwa karatu na biyu a yayin zaman taron na ranar Alhamis.

Kudirin dokar dai da ya wuce zai sauya tanade-tanaden kundin tsarin mulkin Nigeriya, na samar da wa’adin mulki na shekaru shida ga shugaban kasa da gwamnonin jihohi.

Hon. Ikenga Ugochinyere ne ya gabatar da kudirin , Wanda ya bukaci wa’adin mulkin Shugaban kasa da gwamnoni da shugabannin kananan hukumomi ya koma falle daya amma ya kai shekaru shida .

Kudirin ya kuma nemi a ba da damar gudanar da dukkan zabukan shugaban kasa, gwamna da yan majalisu duk a rana daya.

A lokacin da aka kada kuri’a a kan kudirin dokar da aka shirya yi wa karatu na biyu, yawancin ‘yan majalisar sun kada kuri’ar kin amincewa da shi.

Idan za a iya tunawa a kwanakin baya tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya bayar da shawarar a gyara kundin tsarin mulkin kasar na 1999 da dokar zabe ta 2022, saboda a bada dama wa’adin shugaban kasa ya koma na tsawon shekaru shida, sannan a rika baiwa kowacce shiyya dama.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Manyan Tsofaffin Jami'an Soji 10 da Suka Rasa Rayukansu a Hannun ƴan Ta'addaTarihin Rayuwar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaMatsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar AbujaDuk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da 'Yan Ta'adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda - Christopher MusaFarashin ɗanyen Mai ya Faɗi Bayan Amurka ta Soke Sabbin Hare-Haren kaiwa IranAmurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran - TrumpMajalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan JihaHukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar NejaMiyagun ƙwayoyi da Makamai: Jami'an Tsaro Sun Kama Mutane 8 a Jihar YobeAbin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto
X whatsapp