Home General Najeriya ta fara farfaɗowa daga matsin tattalin arziki – Shettima

Najeriya ta fara farfaɗowa daga matsin tattalin arziki – Shettima

Mataimakin shugaban ƙasar Najeriya, Kashim Shettima ya ce Najeriya ta kama hanyar farfaɗowa daga matsalolin matsin tattalin arzikin da take ciki.

Shettima ya ce tattalin arzikin ƙasar na cikin gida wato GDP ya haɓaka da kashi 2.98 a rubu’in farko na wannan shekarar.

Mataimakin shugaban ƙasar ya bayyana hakan ne a lokacin da ya jagoranci tawagar gwamnatin tarayya domin buɗe kasuwar duniya ta Legas ta bana, inda ya ƙara da cewa tsare-tsaren da gwamnatin Tinubu ta ɓullo da su, an yi su ne domin haɓaka tattalin arzikin ƙasar.

Shettima, wanda mai taimaka masa na musamman kan ci gaban yankuna, Dr Marian Tomitope Marshall ta wakilta, ya buƙaci waɗanda za su halarci kasuwar duniyar su yi amfani da damar domin kawo hanyoyin inganta tattalin arziki.

Ya ce gwamnatin Tinubu tana ƙoƙarin samar da hanyoyin sauƙaƙa harkokin kasuwa, domin jin daɗin ƴankasuwa na ciki da wajen ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp