Home General Najeriya ta fara farfaɗowa daga matsin tattalin arziki – Shettima

Najeriya ta fara farfaɗowa daga matsin tattalin arziki – Shettima

Mataimakin shugaban ƙasar Najeriya, Kashim Shettima ya ce Najeriya ta kama hanyar farfaɗowa daga matsalolin matsin tattalin arzikin da take ciki.

Shettima ya ce tattalin arzikin ƙasar na cikin gida wato GDP ya haɓaka da kashi 2.98 a rubu’in farko na wannan shekarar.

Mataimakin shugaban ƙasar ya bayyana hakan ne a lokacin da ya jagoranci tawagar gwamnatin tarayya domin buɗe kasuwar duniya ta Legas ta bana, inda ya ƙara da cewa tsare-tsaren da gwamnatin Tinubu ta ɓullo da su, an yi su ne domin haɓaka tattalin arzikin ƙasar.

Shettima, wanda mai taimaka masa na musamman kan ci gaban yankuna, Dr Marian Tomitope Marshall ta wakilta, ya buƙaci waɗanda za su halarci kasuwar duniyar su yi amfani da damar domin kawo hanyoyin inganta tattalin arziki.

Ya ce gwamnatin Tinubu tana ƙoƙarin samar da hanyoyin sauƙaƙa harkokin kasuwa, domin jin daɗin ƴankasuwa na ciki da wajen ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp