Home General Najeriya ta fara farfaɗowa daga matsin tattalin arziki – Shettima

Najeriya ta fara farfaɗowa daga matsin tattalin arziki – Shettima

Mataimakin shugaban ƙasar Najeriya, Kashim Shettima ya ce Najeriya ta kama hanyar farfaɗowa daga matsalolin matsin tattalin arzikin da take ciki.

Shettima ya ce tattalin arzikin ƙasar na cikin gida wato GDP ya haɓaka da kashi 2.98 a rubu’in farko na wannan shekarar.

Mataimakin shugaban ƙasar ya bayyana hakan ne a lokacin da ya jagoranci tawagar gwamnatin tarayya domin buɗe kasuwar duniya ta Legas ta bana, inda ya ƙara da cewa tsare-tsaren da gwamnatin Tinubu ta ɓullo da su, an yi su ne domin haɓaka tattalin arzikin ƙasar.

Shettima, wanda mai taimaka masa na musamman kan ci gaban yankuna, Dr Marian Tomitope Marshall ta wakilta, ya buƙaci waɗanda za su halarci kasuwar duniyar su yi amfani da damar domin kawo hanyoyin inganta tattalin arziki.

Ya ce gwamnatin Tinubu tana ƙoƙarin samar da hanyoyin sauƙaƙa harkokin kasuwa, domin jin daɗin ƴankasuwa na ciki da wajen ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 
X whatsapp