Home General Tinubu yace zai magance rikicin Manoman da Makiyaya

Tinubu yace zai magance rikicin Manoman da Makiyaya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na baƙin ƙoƙarinta wajen lalubo hanyoyin magance rikice-rikicen manoma da makiyaya.

Yayin da yake jawabi bayan sanya hannu da wasu kamfanin sarrafa nama na JBS a birnin Rio de Janeiro na ƙasar Brazil, Shugaba Tinubu ya ce rikicin manoma da makiyaya ya jima yana haifar da asarar dukiyoyi a wasu yankunan Afirka.

”Rikici tsakanin manoma da makiyaya da ke haifar da asarar rayuka da zubar da jini, idan aka yi amfani da dabarun zamani da wayewa wajen magancenta, zai kawo ci gaban tattalin arzikinmu”, in ji shugaban ƙasar.

Bayan ƙulla yarjejeniyar kamfanin sarrafa nama na JBS ya amince da zuba jarin dala miliyan 2.5 domin gina kamfanonin sarrafa nama shida a faɗin Najeriya.

Kamfanin ya ce uku daga cikin kamfanonin za su mayar da hankali wajen sarar naman kaji, ayayin da biyu za su sarrafa jan nama, sai kuma guda wanda zai sarrafa nama aladu.

Shugaba Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta mayar da hankali wajen gayyato masu zuba jari daga ciki da wajen ƙasar a ɓangaren kiwon dabbobi da noma, lamarin da ya ce zai taimaka wajen magance rikici tsakanin manoman da makiyaya, tare da yaƙar yunwa da talauci da inganta ci gaban tattalin arziki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp