Home General Tinubu yace zai magance rikicin Manoman da Makiyaya

Tinubu yace zai magance rikicin Manoman da Makiyaya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na baƙin ƙoƙarinta wajen lalubo hanyoyin magance rikice-rikicen manoma da makiyaya.

Yayin da yake jawabi bayan sanya hannu da wasu kamfanin sarrafa nama na JBS a birnin Rio de Janeiro na ƙasar Brazil, Shugaba Tinubu ya ce rikicin manoma da makiyaya ya jima yana haifar da asarar dukiyoyi a wasu yankunan Afirka.

”Rikici tsakanin manoma da makiyaya da ke haifar da asarar rayuka da zubar da jini, idan aka yi amfani da dabarun zamani da wayewa wajen magancenta, zai kawo ci gaban tattalin arzikinmu”, in ji shugaban ƙasar.

Bayan ƙulla yarjejeniyar kamfanin sarrafa nama na JBS ya amince da zuba jarin dala miliyan 2.5 domin gina kamfanonin sarrafa nama shida a faɗin Najeriya.

Kamfanin ya ce uku daga cikin kamfanonin za su mayar da hankali wajen sarar naman kaji, ayayin da biyu za su sarrafa jan nama, sai kuma guda wanda zai sarrafa nama aladu.

Shugaba Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta mayar da hankali wajen gayyato masu zuba jari daga ciki da wajen ƙasar a ɓangaren kiwon dabbobi da noma, lamarin da ya ce zai taimaka wajen magance rikici tsakanin manoman da makiyaya, tare da yaƙar yunwa da talauci da inganta ci gaban tattalin arziki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp