Home General Alamu na nuna yiwuwar Najeriya za ta ga ƙarancin mahajjata a bana

Alamu na nuna yiwuwar Najeriya za ta ga ƙarancin mahajjata a bana

Alƙaluma na nuna yiwuwar Najeriya ta fuskanci ƙarancin maniyyata a hajjin bana, wanda ke da nasaba da hauhawar farashin kujerar hajjin bisa bayanan da hukumar kula da aikin hajji ta ƙasar NAHCON ta fitar a rana Litinin.

Hankula sun tashi matuƙa bayan da hukumar aikin hajjin Najeriyar ta fitar da farashin kujerar ta bana wanda ya tasamma miliyan 8 da rabi a wasu yankunan har ya zarta hakan.

Dai dai lokacin da ya rage ƙasa da wata guda kan wa’adin da NAHCON ta bayar wajen kammala biyan kudin aikin hajjin na bana, har yanzu ana ganin ƙarancin mutanen da ke miƙa kuɗinsu don sayen kujerun aikin hajjin na bana wanda alƙaluman ke nuna yiwuwar ya iya zama hajji mafi ƙarancin jama’a daga Najeriyar.

Alƙaluman farashin da NAHCON ta fitar ya nuna cewa mahajjata daga kudancin ƙasar za su biya tsabar kudi har naira miliyan 8 da dubu 700 yayinda maniyyata da arewa maso gabashin Najeriya kuma za su biya naira miliyan 8 da dubu 300 a gefe guda mahajjata daga arewaci kuma za su biya naira miliyan 8 da dubu 400.

Shugaban hukumar ta NAHCON farfesa Abdullahi Saleh Usman ya bayyana cewa hukumar ta yi aiki tuƙuru wajen ganin farashin hajjin a bana bai kai naira miliyan 9 ba.

A baya dai an yi fargabar farashin aikin hajjin a bana ya iya kai naira miliyan 10 musamman lura da karyewar darajar takardar kudi ta Najeriyar naira.

Ƙarƙashin dokokin hukumar NAHCON dai dukkanin maniyyacin da ya gaza biyan adadin kudin aikin hajjin kafin nan da ranar 5 ga watan Fabarairu kai tsaye sai dai ya jira zuwa shekara mai zuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp