Home General Sojoji sun kashe Aminu Kanawa mataimakin Bello Turji

Sojoji sun kashe Aminu Kanawa mataimakin Bello Turji

Sojoji Najeriya da ke yaƙi da ƴanbindiga a arewa maso yammacin Najeriya sun ce sun kashe wani babban mataimakin gawurtaccen ɗanbindigar nan da ke addabar yankin, Bello Turji, mai suna Aminu Kanawa.

A wata sanarwa da sojojin suka fitar ta ce dakarun dai “sun samu nasarar kashe Aminu Kanawa ne lokacin wani samame da suka kai a duwatsun Fakai da ke ƙaramar hukumar Shinkafi.”

“Ɗanbindigar ya yi ƙaurin suna ne wajen addabar al’ummar ƙananan hukumomin jihar ta Zamfara da ma Sokoto da suka haɗa da Zurmi, Shinkafi, Isa da Sabon Birni.”

Sanarwar ta ƙara da cewa baya ga Aminu Kanawa da suka kashe, sojojin sun jikkata ƴanbindiga irin su Dosso wanda ƙanen Turji ne da kuma Danbokolo wanda shi ma makusancinsa ne.

Har wayau, sanarwar ta ƙara da cewa a wani sabon harin da dakarun suka kai sun samu nasarar kashe manyan kwamandojin Bello Turji kamar haka:

  • Abu Dan Shehu
  • Jabbi Dogo
  • Dan Kane
  • Basiru Yellow
  • Kabiru Gebe
  • Bello Buba
  • Dan Inna Kahon-Saniya-Yafi-Bahaushe,

Rundunar sojojin kamar yadda sanarwar ta ce ta samu damar kashe ƙarin kwamandojin Turji guda 24 da ke ƙoƙarin tserewa daga sansanin Turjin da ke Geɓe da Isa.

Sanarwar ta kuma ce dakarun sun kuma kashe wani ɗanbindiga wanda makusancin Halilu Sububu ne yayin kai farmaki a maɓoyar Bello Turjin, mai suna Suleiman.

Daga ƙarshe sanarwar ta ce samun nasarar kashe ƴanbindigar waɗanda ƙasurgumai ne babban rashi ne ga Bello Turji wanda “nan gaba kaɗan zai zama cikin komarmu”.

Kafar watsa labarai ta PR Nigeria ta wallafa cewa wata majiya daga hedkwatar tsaro ta Najeriya ta tabbatar mata da tserewar Turji zuwa yankin Maradun, sannan mutanen yankin sun tabbatar da ganin wasu babura suna zarya, waɗanda ake tunanin sun ɗauki ƴanbindiga da aka harba ne suna tafiya da su zuwa yankin Kadanya da Bayan Ruwa.

Ko a ranar Talata sai da sojojin suka bayar da sanarwar kashe ɗangidan Bello Turji yayin wani samame da suka kai sansanin ɗanbindigar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar Benue
X whatsapp