Home General Likitoci sun shiga yajin aiki a asibitocin Abuja

Likitoci sun shiga yajin aiki a asibitocin Abuja

Likitoci masu neman ƙwarewa sun shiga yajin aiki a Abuja, saboda rashin biyansu albashi da kuɗaɗen alawus da sauran buƙatunsu.

A wani taron manema labarai da ƙungiyar ta gudanar yau Laraba, a babban birnin Najeriyar, shugaban ƙungiyar, Dr George Ebong, ya ce yajin aikin na gargaɗi ne kuma kuma za su yi shi ne tsawon kwana uku.

Yajin aikin dai ya durƙusar da ayyuka a asibitocin gwamnati a birnin na tarayya.

Ebong ya ce sun shiga yajin aikin ne bayan ƙarewar wa’adin mako uku da suka ba gwamnati na gargaɗi.

Ƙungiyar ta koka da abin da ta ce wasarere da rashin kula da asibitoci da aka yi a Abuja.

Shugaban ya buƙaci ministan Abuja, Nyesome Wike da ya shiga lamarin don gujewa shiga yajin aikin sai-abin- da-hali ya yi.

A ranar Talata ne ƙungiyar likitoci ta yanke shawarar tsunduma yajin aikin bayan taron shugabanninta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp