Home General Likitoci sun shiga yajin aiki a asibitocin Abuja

Likitoci sun shiga yajin aiki a asibitocin Abuja

Likitoci masu neman ƙwarewa sun shiga yajin aiki a Abuja, saboda rashin biyansu albashi da kuɗaɗen alawus da sauran buƙatunsu.

A wani taron manema labarai da ƙungiyar ta gudanar yau Laraba, a babban birnin Najeriyar, shugaban ƙungiyar, Dr George Ebong, ya ce yajin aikin na gargaɗi ne kuma kuma za su yi shi ne tsawon kwana uku.

Yajin aikin dai ya durƙusar da ayyuka a asibitocin gwamnati a birnin na tarayya.

Ebong ya ce sun shiga yajin aikin ne bayan ƙarewar wa’adin mako uku da suka ba gwamnati na gargaɗi.

Ƙungiyar ta koka da abin da ta ce wasarere da rashin kula da asibitoci da aka yi a Abuja.

Shugaban ya buƙaci ministan Abuja, Nyesome Wike da ya shiga lamarin don gujewa shiga yajin aikin sai-abin- da-hali ya yi.

A ranar Talata ne ƙungiyar likitoci ta yanke shawarar tsunduma yajin aikin bayan taron shugabanninta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp