Home General Likitoci sun shiga yajin aiki a asibitocin Abuja

Likitoci sun shiga yajin aiki a asibitocin Abuja

Likitoci masu neman ƙwarewa sun shiga yajin aiki a Abuja, saboda rashin biyansu albashi da kuɗaɗen alawus da sauran buƙatunsu.

A wani taron manema labarai da ƙungiyar ta gudanar yau Laraba, a babban birnin Najeriyar, shugaban ƙungiyar, Dr George Ebong, ya ce yajin aikin na gargaɗi ne kuma kuma za su yi shi ne tsawon kwana uku.

Yajin aikin dai ya durƙusar da ayyuka a asibitocin gwamnati a birnin na tarayya.

Ebong ya ce sun shiga yajin aikin ne bayan ƙarewar wa’adin mako uku da suka ba gwamnati na gargaɗi.

Ƙungiyar ta koka da abin da ta ce wasarere da rashin kula da asibitoci da aka yi a Abuja.

Shugaban ya buƙaci ministan Abuja, Nyesome Wike da ya shiga lamarin don gujewa shiga yajin aikin sai-abin- da-hali ya yi.

A ranar Talata ne ƙungiyar likitoci ta yanke shawarar tsunduma yajin aikin bayan taron shugabanninta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man Kan Sayar da Farashin FeturNECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin Najeriya
X whatsapp