Home General NLC Ta Buƙaci Ministan Makamashi Ya Sauka Daga Mukaminsa

NLC Ta Buƙaci Ministan Makamashi Ya Sauka Daga Mukaminsa

Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya (NLC), ta yi kira ga Ministan Makamashi, Adebayo Adelabu da ya sauka daga mukaminsa saboda yawaitar katsewar babban layin lantarki na ƙasa.

A wata sanarwa da shugaban ƙungiyar, Joe Ajaero ya fitar, ya ce ƙungiyar na takaicin yadda ɓangaren lantarkin Najeriya ya ƙi gyaruwa, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

A cewar Ajaero, “Idan har akwai ma’aikata ƙwararru waɗanda suka san makamar aiki a ma’aikatar makamashi, to lallai za’a iya kiyaye yawaitar abin kunyar nan da ake fuskanta na yawaitar katsewar layin lantarki a Najeriya. Magance matsalar ya kamata ministan ya yi, ba ya riƙa maganar cewa za su magance ta ba.

“Mun yi amannar cewa wannan ya nuna rashin ƙwarewa da gazawar ma’aikatar makamashin, wanda hakan ya sa muke mamakin me ya sa wanda ke jagorantar ma’aikatar ba zai sauka cikin mutunci ba”.

A karshe Ajaero ya kuma caccaki ministan bisa kasafta kashe naira biliyan 8 a kasafin kuɗin 2025 domin “wayar da kan ƴan Najeriya muhimmancin biyan kuɗin lantarki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp