Home General Najeriya za ta samar da lantarki ta hasken rana ga wasu jihohin...

Najeriya za ta samar da lantarki ta hasken rana ga wasu jihohin arewa 19

Gwamnatin Najeriya ta bayyana shirinta na gina tashoshin samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana mai karfin megawatt 1,900 ga jihohin arewa 19, a wani bangare na ƙoƙarin bunkasa makamashin mara gurbata muhalli da kuma faɗaɗa cibiyoyin samar da lantarki ta ƙasa

Ministan Wutar Lantarkin Najeriya, Adebayo Adelabu, ne ya bayyana hakan a yayin taron manema labarai karo na shida na 2025 da aka gudanar ranar Alhamis a Abuja, inda ya bayyana burin gwamnati na samar da kusan MW 8,000 na wutar lantarki kafin ƙarshen wa’adin mulkin Shugaba Bola Tinubu na farko a shekarar 2027.

Adelabu ya ce kowace tasha mai amfani da hasken rana za ta samar da kusan megawatt 100 na wutar lantarki, wanda hakan zai baiwa jihohi damar dogaro da kai da kuma rage dogaro da babbar cibiyar samar da wutar lantarki ta ƙasa.

Ya kuma bayyana cewa gwamnati na bin diddigin samun masu saka hannun jari masu zaman kansu don taimakawa wajen faɗaɗa babbar cibiyar lantarki ta ƙasa tare zamanantar da ita.

Wannan na zuwa ne daidai lokacin da ƴan Najeriya ke nuna damuwa dangane da yadda babbar cibiyar samar da lantarki ta ƙasa ke lalacewa tare da jefa ƙasa baki ɗaya cikin dubu a baya-bayan nan, musaman yankin arewa da ya fuskanci kalubale ta hanyar katsawar lantaki da aka alakanta da bata gari da ke lalata turakun wutan lantarki da kuma sata kayayyaki masu muhimmaci.

A watan Oktoban da ya gabata, barayin sun lalata muhimmin layin wutar lantarki na Shiroro zuwa Kaduna mai karfin 330kV da ke samarwa jihohin Kano da Kaduna, da kuma wani layin da ke samar da Bauchi da Gombe da sauran sassan arewa maso gabas wuta.

Wannan lamari dai ya haifar da bacin rai na tsawon wata guda a jihohi 17 cikin 19 na arewacin ƙasar. Bayan gyare-gyaren, gwamnonin jihohin Arewa 19 sun yi kira da a samar da wutar lantarki masu zaman kansu ga jihohin domin tabbatar da ingantacciyar wutar lantarki a yankin.

Jihohin sun hada da Neja da Kwara da Kaduna da Kano da Jigawa daGombe da Katsina. Sauran sun hada da Sokoto da Zamfara da Bauchi da Yobe da Borno da Adamawa da Taraba da Naija da Filato da Nasarawa da Kogi da kuma Benue.

Sai dai da yake jawabi a wurin taron da kuma bayyana nasarorin da aka samu kawo yanzu, ministan ya jaddada cewa duba da hasken rana da Allah ya albarkaci Najeriya, babu dalilin da zai sa ƙasar ba za ta iya samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp