Home General Ba a hana Kashim Shettima shiga Villa ba – Fadar Shugaban Najeriya

Ba a hana Kashim Shettima shiga Villa ba – Fadar Shugaban Najeriya

Fadar shugaban Najeriya, ta musanta wasu rahotonnin da ke zargin cewa an hana mataimakin shugaban ƙasar, Kashim Shettima shiga fadar shugaban ƙasar ta Villa.

A ƴan kwanakin nan an yi ta yaɗa jita-jitar cewa jami’an tsaro sun hana mataimakin shugaban ƙasar shiga fadar shugaban ƙasar.

To sai dai cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasar, da ke aiki da ofishin mataimakin shugaban ƙasar, Stanley Nkwocha ya fitar, ya ce labarin ba shi da tushe balle makama, ”ƙarya ce tsagwaronta da aka shirya domin nuna wa jama’a cewa akwai saɓani tsakanin manyan jami’an gwamnatin”.

”An shirya wannan labarin ƙarya ne domin haddasa ruɗani da saɓani a fadar shugaban ƙasa, haka kuma labari ne da ke son haddasa ruɗani a zukatan ƴanƙasa”, in ji sanarwar.

Fadar shugaban ƙasar ta ce ta fahimci masu yaɗa labaran ƙarya ne ke son raba kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin shugaban ƙasar da mataimakin nasa, kuma haƙarsu ba za ta cimma ruwa ba, kamar yadda fadar ta bayyana.

Sanarwar ta ce matamakin shugaban ƙasar na mayar da hankalinsa kan ayyukan da ke gabansa na tallafa wa shugaban ƙasa wajen ciyar da Najeriya gaba, don haka ba ma shi da lokacin ɓatawa.

Daga ƙarshe sanarwar ta yi kira ga al’umma su yi watsi da labaran da suka fito da majiyoyi marasa tushe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp