Home General Ba a hana Kashim Shettima shiga Villa ba – Fadar Shugaban Najeriya

Ba a hana Kashim Shettima shiga Villa ba – Fadar Shugaban Najeriya

Fadar shugaban Najeriya, ta musanta wasu rahotonnin da ke zargin cewa an hana mataimakin shugaban ƙasar, Kashim Shettima shiga fadar shugaban ƙasar ta Villa.

A ƴan kwanakin nan an yi ta yaɗa jita-jitar cewa jami’an tsaro sun hana mataimakin shugaban ƙasar shiga fadar shugaban ƙasar.

To sai dai cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasar, da ke aiki da ofishin mataimakin shugaban ƙasar, Stanley Nkwocha ya fitar, ya ce labarin ba shi da tushe balle makama, ”ƙarya ce tsagwaronta da aka shirya domin nuna wa jama’a cewa akwai saɓani tsakanin manyan jami’an gwamnatin”.

”An shirya wannan labarin ƙarya ne domin haddasa ruɗani da saɓani a fadar shugaban ƙasa, haka kuma labari ne da ke son haddasa ruɗani a zukatan ƴanƙasa”, in ji sanarwar.

Fadar shugaban ƙasar ta ce ta fahimci masu yaɗa labaran ƙarya ne ke son raba kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin shugaban ƙasar da mataimakin nasa, kuma haƙarsu ba za ta cimma ruwa ba, kamar yadda fadar ta bayyana.

Sanarwar ta ce matamakin shugaban ƙasar na mayar da hankalinsa kan ayyukan da ke gabansa na tallafa wa shugaban ƙasa wajen ciyar da Najeriya gaba, don haka ba ma shi da lokacin ɓatawa.

Daga ƙarshe sanarwar ta yi kira ga al’umma su yi watsi da labaran da suka fito da majiyoyi marasa tushe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp