Home General Natasha ta bukaci a dawo mata da Jami’an tsaron da ak janye...

Natasha ta bukaci a dawo mata da Jami’an tsaron da ak janye mata

Ƴar Majalisar Dattawan Najeriya, mai wakilitar Kogi ta Tsakiya, Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan – da aka dakatar – ta yi kira ga babban sifeton ƴansandan ƙasar, ya mayar mata da jami’an tsaronta da aka janye mata lokacin da majalisa ta dakatar da ita.

Kiran na zuwa ne bayan da wasu mahara suka auka wa gidan kakanninta da ke jihar Kogi ranar Talatar da ta gabata.

Jaridun Najeriya sun ambato wata sanarwa da ofishin yaɗa labaran ƴar majalisar ya fitar, na cewa an kai harin ne a lokacin da ƙaninta ya je garin domin duba wani aikin mazaɓu da Natasha ke gudanarwa a garinta na Obeiba-Ihima.

Sanata Natasha ta yi zargin cewa ita aka ƙudiri aniyar kai wa harin, tana mai cewa maharan sun kai harin ne saboda a tunaninsu tana gidan.

Harin ya lalata wasu ɓangarorin gidan, wanda ƴar majalisar ta ce na kakanta ne.

To sai dai jami’an tsaro sun yi asarar daƙile harin, kamar yadda ta yi ƙarin haske.

A watan da ya gabata ne dai Majalisar Dattawan Najeriyar ta dakatar da ƴar majalisar tsawo wata shida, tare da tsayar da alawus-alawus da ake ba ta da jami’an tsaron da ke ba ta kariya, saboda zargin rashin ɗa’a.

Dakatarwar na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan ta zargi Shugaban Majalisar Dattawan Ƙasar, Sanata Godswill Akpabio da yunƙurin cin zarafi na lalata da amfani da ofishinsa wajen tursasawa da kuma daƙile mata aikinta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp