Home Labarai SEAMA ta karrama Shugaban NDLEA, da wasu Manyan Jami’an tsaro

SEAMA ta karrama Shugaban NDLEA, da wasu Manyan Jami’an tsaro

An karrama Shugaban hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta NDLEA, da washu shuwagabnnin hukumomin tsaro a Nijeriya da lambar yabo.

Wannan na zuwa ne a yayin taron SEAMA karo na 7, tare da taron bayar da lambar yabo don tsaro da taimakon gaggawa (SEAMA 2025); a taron an karrama mayyana jamián tsaro bisa gudunmawar da suka bayar ga Al’uamma da kasa baki daya.

Taron da jaridar Emergency Digest, dake karkashin rukunin kafanin yada labarai na Image Merchants Promotion Limited – IMPR) bisa hadin gwiwar cibiyar dakile yaduwar rikice –rikice ta fannin sadarwa wato CCC, da CISLAC da kuma kungiyar TIEMS ya bayyana nasarorin da aka samu a shekarar da ta gabata.

A yayin taron shugaban hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyin Birgediya Janar Bubu Marwa mai ritaya ya rabauta da lamabar yabo da “fitaccen shugaba” bisa irin yadda ya jagorancin kawo sauye –sauye a fannin yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a Nijeriya.

A karkashin jagorancinsa, hukumar NDLEA ta fatattaki ƙungiyoyin dillalan ƙwayoyi, ta ƙarfafa binciken leƙen asiri, tare da wayar da kai kan illolin ƙwayoyi karkashin shirin WADA.

ko dai a ‘yan tsakankanin nan shugaba Tinubu ya tabbatar da karin wa’adinsa na shekaru biyar bisa gudummawar da hukumar ta bayar wajen tsaro.

Daga cikin wadanda aka karrama, daraktan yada labaran hukumar ta NDLEA Femi Babafemi, matsayin “Fitaccen Jami’in Wayar da Kan Jama’a a Lokacin Rikici”. Bisa ayyukansa na wallafa bayanai, bayyana nasarorin kama miyagun ƙwayoyi da masu fatauci, da kuma gyara bayanan da ke rikita jama’a, domin tabbatar da sun ƙara inganta suna da sahihancin daga hukumar.

A watan Satumbar 2025, ya bayyana sakin wasu ‘yan Najeriya uku da aka tsare a kasar Saudiyya ba bisa ka’ida ba — abin da ya nuna jajircewarsa ga adalci da ingantacciyar sadarwa.

Sai kuma Kwamandan hukumar NSCDC na birnin Abuja, Olusola Odumosu, wanda ya sami lambar yabo ta “Jami’in Tsaro na Shekara” saboda kwazonsa wajen magance laifuka, kama masu fasa kwauri da masu barna a babban birnin tarayya.

Haka kuma, Kwamishinan ‘Yan Sanda na Legas, CP Olohundare Moshood Jimoh, ya samu lambar yabo ta “Jami’in ‘Yan Sanda na Shekara” saboda yadda ya tarwatsa manyan ƙungiyoyin laifi, musamman a Ikorodu da Shomolu, ta hanyar amfani da bayanan sirri don hana aikata laifi da kakkabe ayyukan ‘yan ƙungiya.

Kwamodo Omobamidele Adetokunbo Akinbami, Kwamandan NNS SOROH, shi ne “Jami’in Soja na Shekara” saboda yaki da fashin teku, lalata bututun mai, da karancin mai a jihohin kudanci. Daga Mayu 2024 zuwa Afrilu 2025, rundunarsa ta rushe haramtattun matatun mai guda 145, ta kama jiragen ruwa, ta kwato danyen mai da dizal da aka sace, tare da lalata sansanonin ‘yan bindiga a yankunan ruwa.

Daga cikin sauran mutanen da aka karrama akwai Rahila Lassa Garba daga Voice of Nigeria (VON), wadda ta samu yabo kan aikin jarida na jinƙai da yake fayyace halin da al’ummar da ke cikin mawuyacin hali ke ciki, tare da jawo daukar matakan tallafi.

A bangaren hukumomi kuwa, DSS ta samu lambar yabo kan “Magance Laifi”, yayin da Hukumar Kwastam (NCS) ta samu yabo kan “Gudanar da Bayanai da Wayar da Kan Jama’a” saboda yadda take fitar da bayanai cikin gaskiya da kauce wa yaɗuwar jita-jita. EFCC ta samu yabo wajen “Rigakafin Laifukan Sadarwa (Cybercrime)”, FRSC kan “Ceton Gaggawa”, yayin da Yobe SEMA ta samu yabo kan “Ayyukan Jinƙai”.

Sauran hukumomin da aka karrama sun haɗa da: Rundunar Sojin Najeriya (NA) saboda ayyukan CIMIC, ICPC saboda tsantseni wajen bincike, da NAF saboda inganta alaƙar soji da jama’a ta hanyar ayyukan jinƙai. Makarantar Horas da Ma’aikatan Gidajen Gyara Hali ta Kaduna ta zama “Makarantar Horaswa ta Shekara”.

Taron ya kuma jaddada muhimmancin haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro, kafafen yada labarai, da kungiyoyin farar hula wajen kare Najeriya da inganta wayar da kai ga jama’a. SAEMA 2025 ta nuna yadda karramawa kan nagarta ke ƙarfafa jajircewa wajen yaki da laifuka da kare rayuka.

PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp