Home Labarai Na kadu matuka da sace Dalibai ‘yan mata a jihar Kebbi –...

Na kadu matuka da sace Dalibai ‘yan mata a jihar Kebbi – Tinubu

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce yana takaicin sace ƴan matan da aka yi a Kebbi, da kuma alhinin mutuwar Birgadiya Janar Musa Uba da gwarazan sojojin da suka mutu a jihar Borno.

A cikin wani saƙon da ya wallafa a shafinsa na X, Tinubu ya ce ya shiga matuƙar damuwa kan mutuwar sojojin ƙasar da ke bakin aiki.

Ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu, da kuma saƙon jaje da iyayen ɗaliban da aka sace, inda ya ce yana ci gaba da yi musu addua.

” Ina cikin damuwa sosai kan yadda ƴan bindiga suka katse wa ƴan matan nan karatunsu, na umurci jam’ian tsaro su yi gaggawar dawo da ƴan matan gida” ” Ina sane da ƙaruwar rashin tsaro a wasu sassan ƙasar, kuma na bai wa jami’an tsaro umurnin daƙile matsalolin cikin gaggawa”. a cewar shugaban.

Ya kuma yi kira ga ƴan ƙasar da su taimaka wa jam’ian tsaro wajen basu haɗin kai da kuma bayanai masu muhimmanci, inda ya sha alwashin hukunta masu yi wa tsaron ƙasar barazana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp