Home Labarai Kwankwaso ya nuna damuwarsa bisa sake dawowar rashin tsaro a Nijeriya

Kwankwaso ya nuna damuwarsa bisa sake dawowar rashin tsaro a Nijeriya

Jagoran jam’iyyar NNPP a Najeriya Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ce ƙaruwar hare-hare da ake samu na baya-bayan nan a ƙasar ya kai matakin da ke buƙatar matakin gaggawa daga hukumomi, musamman daga gwamnatin ƙasar.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na X, Kwankwaso ya ce wajibi ne gwamnatin Najeriya ta sauke babban nauyin da ke kanta na kare rayukan al’umma, ta hanyar ƙarfafa wa jam’ian tsaron ƙasar gwiwa.

”Da farko, sace ɗalibai ƴanmata 25 a Kebbi abin damuwa ne da ke sanya fargabar ko za a maimaita abin da ya faru a baya, sai sacewa da kuma kashe Birgadiya janar M Uba da ƴan ta’adda suka yi a Borno, wanda yana daga cikin lokuta mafi muni a yaƙin da ƙasar ke yi da ta’addanci,” in ji shi.

Ya kuma nuna damuwa game da sace gwamman mutane a Zamfara, da kuma ƙaruwar harin da ƴan bindiga ke kai wa a ƙananan hukumomin Shanono da Ghari a jihar Kano.

”Ina kira a yi gaggawar ceto waɗanda aka sace, domin hare-haren baya-bayan nan na nuna koma baya a yaƙin da ake yi da matsalar tsaro,” a cewar sa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp