Home Labarai Kwankwaso ya nuna damuwarsa bisa sake dawowar rashin tsaro a Nijeriya

Kwankwaso ya nuna damuwarsa bisa sake dawowar rashin tsaro a Nijeriya

Jagoran jam’iyyar NNPP a Najeriya Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ce ƙaruwar hare-hare da ake samu na baya-bayan nan a ƙasar ya kai matakin da ke buƙatar matakin gaggawa daga hukumomi, musamman daga gwamnatin ƙasar.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na X, Kwankwaso ya ce wajibi ne gwamnatin Najeriya ta sauke babban nauyin da ke kanta na kare rayukan al’umma, ta hanyar ƙarfafa wa jam’ian tsaron ƙasar gwiwa.

”Da farko, sace ɗalibai ƴanmata 25 a Kebbi abin damuwa ne da ke sanya fargabar ko za a maimaita abin da ya faru a baya, sai sacewa da kuma kashe Birgadiya janar M Uba da ƴan ta’adda suka yi a Borno, wanda yana daga cikin lokuta mafi muni a yaƙin da ƙasar ke yi da ta’addanci,” in ji shi.

Ya kuma nuna damuwa game da sace gwamman mutane a Zamfara, da kuma ƙaruwar harin da ƴan bindiga ke kai wa a ƙananan hukumomin Shanono da Ghari a jihar Kano.

”Ina kira a yi gaggawar ceto waɗanda aka sace, domin hare-haren baya-bayan nan na nuna koma baya a yaƙin da ake yi da matsalar tsaro,” a cewar sa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp