Home Labarai Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya fice daga Jam’iyyar NNPP

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya fice daga Jam’iyyar NNPP

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar NNPP, yana mai danganta matakin da rikice-rikicen cikin gida da suka dabaibaye jam’iyyar, tare da cewa ya dauki wannan mataki ne domin kare muradun al’ummar jihar Kano.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya rattaba wa hannu kuma aka rabawa manema labarai a jihar ranar Juma’a.

A wata wasika da gwamnan ya aike wa shugaban jam’iyyar NNPP na mazabarsa ta Diso-Chiranchi dake Karamar Hukumar Gwale, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar tun daga yau Juma’a, 23 ga Janairu, 2026.

A cewar gwamnan, “Na rubuto wannan wasika ne cike da godiya domin sanar da shugabancin jam’iyyar NNPP matsayina na ficewa daga jam’iyyar, wanda zai fara aiki daga ranar Juma’a, 23 ga Janairu, 2026.”

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nuna godiyarsa ga jam’iyyar bisa damar da ta ba shi da kuma goyon bayan da ya samu tun bayan shigarsa jam’iyyar a shekarar 2022.

Gwamnan ya ce jam’iyyar na fama da rikice-rikicen cikin gida, sakamakon sabanin shugabanci da kuma shari’o’i da dama da ke gaban kotuna a sassa daban-daban na kasar nan.

A cewarsa, wadannan rikice-rikice sun haifar da rarrabuwar kai da raunana dunkulewar jam’iyyar a matakin jiha da kasa baki daya.

Gwamna Yusuf ya bayyana cewa bayan yin nazari mai zurfi, ya yanke shawarar ficewa daga jam’iyyar ne bisa la’akari da muradun jama’a.

Gwamnan ya jaddada cewa ya dauki matakin ne da kyakkyawar niyya, ba tare da wata gaba ko kiyayya ba, yana mai tabbatar da kudirinsa na ci gaba da wanzar da zaman lafiya, hadin kai da ci gaban jihar Kano.

Rahotanni sun nuna cewa gwamnan ya fice daga jam’iyyar tare da mambobi 21 na Majalisar Dokokin Jihar Kano, mambobi 8 na Majalisar Wakilai ta kasa, da kuma shugabannin kananan hukumomi 44 na jihar.

Sakataren jam’iyyar NNPP na mazabar Diso-Chiranchi, Honarabul Kabiru Zubairu, ya tabbatar da karbar wasikar ficewar gwamnan, inda ya yaba masa bisa ayyukan raya kasa da ya aiwatar, musamman a bangarorin ababen more rayuwa, gyaran birane, lafiya, ilimi da bunkasa tattalin arziki.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp