Home Labarai Amurka na son Najeriya ta ƙara jajircewa wajen kare Kiristoci

Amurka na son Najeriya ta ƙara jajircewa wajen kare Kiristoci

Amurka da Najeriya sun yi taron farko a Abuja domin ƙarfafa hadin gwiwar tsaro da kare fararen hula daga ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai ƴanbindiga.

Taron dai an yi shi ne da nufin tabbatar da cewa dukkan mabiya addinai za su iya gudanar da addininsu cikin aminci.

Hakan ya biyo bayan ayyana Najeriya a matsayin ƙasar da ake da damuwa a kanta, musamman saboda kisan kiyashin da ake zargin ana yi wa kiristoci, ikirarin da hukumomin Najeriyar suka musanta.

Amurka ta yi maraba da ƙoƙarin Najeriya na magance matsalar rashin tsaro, musamman a jihohin Arewa ta tsakiya.

Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu ne ya jagoranci tawagar Najeriyar da ta ƙunshi ma’aikatu da hukumomi 10, yayin da mataimakiyar sakataren harkokin wajen Amurka Allison Hooker ta jagoranci tawagar Amurka da ke da wakilaiu daga hukumomin tarayya takwas.

Sanarwar hadin gwiwa da aka fitar ranar Alhamis ta jaddada ƙudurin gwamnatocin biyu na tabbatar da ƴancin addini da kare ƴancin faɗin albarkacin baki da gudanar da taron lumana.

Sanarwar ta ƙara da cewa, ‘’Tawagar ta Amurka ta godewa Najeriya kan matakan gaggawa da ta ɗauka na ƙarfafa tsaro ga al’ummomin Kirista da mabiyan sauran addinai da ke cikin haɗari sakamakon ayyukan ta’addanci.”

Ƙasashen biyu dai na musayar bayanan sirri domin tunkarar matsalar ta’addanci daga ƙungiyoyi masu iƙirarin jihadi da ya yi sanadin mutuwar dubban mutane tare da raba miliyoyi da muhallansu a arewacin Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp