Home Labarai Amurka na son Najeriya ta ƙara jajircewa wajen kare Kiristoci

Amurka na son Najeriya ta ƙara jajircewa wajen kare Kiristoci

Amurka da Najeriya sun yi taron farko a Abuja domin ƙarfafa hadin gwiwar tsaro da kare fararen hula daga ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai ƴanbindiga.

Taron dai an yi shi ne da nufin tabbatar da cewa dukkan mabiya addinai za su iya gudanar da addininsu cikin aminci.

Hakan ya biyo bayan ayyana Najeriya a matsayin ƙasar da ake da damuwa a kanta, musamman saboda kisan kiyashin da ake zargin ana yi wa kiristoci, ikirarin da hukumomin Najeriyar suka musanta.

Amurka ta yi maraba da ƙoƙarin Najeriya na magance matsalar rashin tsaro, musamman a jihohin Arewa ta tsakiya.

Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu ne ya jagoranci tawagar Najeriyar da ta ƙunshi ma’aikatu da hukumomi 10, yayin da mataimakiyar sakataren harkokin wajen Amurka Allison Hooker ta jagoranci tawagar Amurka da ke da wakilaiu daga hukumomin tarayya takwas.

Sanarwar hadin gwiwa da aka fitar ranar Alhamis ta jaddada ƙudurin gwamnatocin biyu na tabbatar da ƴancin addini da kare ƴancin faɗin albarkacin baki da gudanar da taron lumana.

Sanarwar ta ƙara da cewa, ‘’Tawagar ta Amurka ta godewa Najeriya kan matakan gaggawa da ta ɗauka na ƙarfafa tsaro ga al’ummomin Kirista da mabiyan sauran addinai da ke cikin haɗari sakamakon ayyukan ta’addanci.”

Ƙasashen biyu dai na musayar bayanan sirri domin tunkarar matsalar ta’addanci daga ƙungiyoyi masu iƙirarin jihadi da ya yi sanadin mutuwar dubban mutane tare da raba miliyoyi da muhallansu a arewacin Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp