Home Labarai Shugaba Tinubu ya nada Jakadan da zai wakilci Nijeriya a Amurka

Shugaba Tinubu ya nada Jakadan da zai wakilci Nijeriya a Amurka

Shugaba Bola Tinubu ya amince da nadin jakadu hudu, daga cikin 68 da Majalisar Dattawa ta amince da su a watan Disamban 2025.Tinubu ya tabbatar da nadin Ayodele Oke a matsayin jakadan da aka nada a Faransa, da kuma Lateef Are a matsayin jakadan da aka nada a Amurka.

Shugaban Najeriya ya kuma tabbatar da nadin Amin Dalhatu, tsohon jakadan Korea ta Kudu, a matsayin babban kwamishina da aka nada a Birtaniya.

Usman Isa Dakingari Suleiman, tsohon gwamnan Kebbi, shi ne jakadan da aka nada a Turkiyya,ƙasar da Shugaba Tinubu zai fara ziyara a mako na sama.

A cikin wata sanarwa da ya aike wa Ma’aikatar Harkokin Waje, Shugaba Tinubu ya bukaci ma’aikatar ta sanar da gwamnatocin kasashen hudu game da nadin jakadun, bisa ga tsarin diflomasiyya.

Mai baiwa shugaba Tinubu shawara kan dabaru da hulda da manema labarai Bayo Onanuga,ya jaddada manufar shugaba Tinubu na ganin Najeriya ta shiga sahun manyan ƙasashe a fanin diflomasiyya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp