Home Labarai Shugaba Tinubu ya nada Jakadan da zai wakilci Nijeriya a Amurka

Shugaba Tinubu ya nada Jakadan da zai wakilci Nijeriya a Amurka

Bola Ahned Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya amince da nadin jakadu hudu, daga cikin 68 da Majalisar Dattawa ta amince da su a watan Disamban 2025.Tinubu ya tabbatar da nadin Ayodele Oke a matsayin jakadan da aka nada a Faransa, da kuma Lateef Are a matsayin jakadan da aka nada a Amurka.

Shugaban Najeriya ya kuma tabbatar da nadin Amin Dalhatu, tsohon jakadan Korea ta Kudu, a matsayin babban kwamishina da aka nada a Birtaniya.

Usman Isa Dakingari Suleiman, tsohon gwamnan Kebbi, shi ne jakadan da aka nada a Turkiyya,ƙasar da Shugaba Tinubu zai fara ziyara a mako na sama.

A cikin wata sanarwa da ya aike wa Ma’aikatar Harkokin Waje, Shugaba Tinubu ya bukaci ma’aikatar ta sanar da gwamnatocin kasashen hudu game da nadin jakadun, bisa ga tsarin diflomasiyya.

Mai baiwa shugaba Tinubu shawara kan dabaru da hulda da manema labarai Bayo Onanuga,ya jaddada manufar shugaba Tinubu na ganin Najeriya ta shiga sahun manyan ƙasashe a fanin diflomasiyya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp