Home Labarai rahotannin daga jihar Katsina na cewa ‘Yan bindiga sun kashe mutum 9...

rahotannin daga jihar Katsina na cewa ‘Yan bindiga sun kashe mutum 9 a jihar

Ana ci gaba da zaman ɗar-ɗar a garuruwan Kauran Fawa da Unguwar Jika, da wasu garuruwa a ƙaramar hukumar Ɗan Ɗume a Jihar Katsina, bayan wani hari da wasu ’yan bindiga suka kai inda ake fargabar sun kashe mutum tara, tare da jikkata wasu 13.

Harin wanda aka kai cikin daren Alhamis na zuwa ne duk da sulhun da masu ruwa da tsaki a yankin suka jagoranta da ’yan bindigar, a wani yunƙuri na dawo da zaman lafiya da kare rayuka da kuma dukiyoyin al’umma.

Sai dai, hukumomin yankin sun ce sun halarci jana’izar mutum biyar, kuma suna ci gaba da ɗaukar matakai domin dawo da zaman lafiya.

Wani mazaunin ɗaya daga cikin garuruwan da abin ya shafa, wanda ya buƙaci a sakaya sunansa, ya shaida wa manema labarai cewa ƴanbindigar sun shiga garin ne a ƙafa inda suka yi ta harbi.

“Mutum tara ne suka mutu sakamakon harbin da yanbindigar suka yi, sannan 13 ne suka samu raunuka inda muka kai su asibiti domin samun kulawa. Sun ɗauki mutum aƙalla goma amma sai suka yi ta sakin mutanen sakamakon artabu. Mutum ɗaya ne ya rage a hannun su,” in ji shi.

Shugaban karamar hukumar Ɗan Dume, Bishir Hadi, ya tabbatar da afkuwar lamarin, inda ya ce tare da shi aka yi jana’izar mutanen da aka kashe.

“Mun yi sulhu kuma mun samu nasara, tsawon wata biyar ba a kawo hari ba sai yanzu. Kafin yanzu babu ranar da ba a kawo mana hari,” in ji Bishir.

Jihar Katsina da ke arewa maso yammacin Najeriya ta daɗe tana fama da hare-haren ’yan bindiga.

Duk da sulhun da gwamnatin jihar ta yi da ƴanbindigar tare da sakin wasu da aka kama, amma hukumomin na cewa matakin na daga cikin yarjejeniyoyin da wasu al’ummomin jihar suka amince da su domin samun zaman lafiya mai ɗorewa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp