Home Taska Jami’an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da Lakurawa

Jami’an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da Lakurawa

Jami’an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da Lakurawa

 

Jami’an hukumar kwastam biyu sun rasa ransu a fafatawar da suka yi da mayaƙan da ake zargi Lakurawa ne a jihar Kebbi.

Shugaban hukumar kwastam, Bashir Adeniyi, ya ce lamarin ya faru ne da safiyar ranar Laraba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa jami’an masu muƙamin ASC da DSC, sun rasa ransu ne yayin samamen yaƙi da ƴan ta’adda da tsakiyar dare.

Adeniyi ya faɗi hakan ne a birnin Illorin yayin da yake gabatar da jawabi a jami’ar Illorin da ke jihar Kwara.

Rahotanni sun ce maharan sun farwa shingen binciken ababen hawa na tsaro da ke kusa da juna.

A nan ne kuma suka harbi jami’i guda sannan suka cinna wa ɗaya jami’in wuta da ransa.

Gwamnan jihar Kwara, AbdurRahman AbdulRazaq ya miƙa saƙon ta’aziyyarsa ga hukumar ta kwastam kan mutuwar jami’an biyu inda ya bayyana su a matsayin ƴan kishin ƙasa da suka rasa ransu yayin hidimta wa ƙasarsu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp