Home Taska Jami’an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da Lakurawa

Jami’an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da Lakurawa

Jami’an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da Lakurawa

 

Jami’an hukumar kwastam biyu sun rasa ransu a fafatawar da suka yi da mayaƙan da ake zargi Lakurawa ne a jihar Kebbi.

Shugaban hukumar kwastam, Bashir Adeniyi, ya ce lamarin ya faru ne da safiyar ranar Laraba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa jami’an masu muƙamin ASC da DSC, sun rasa ransu ne yayin samamen yaƙi da ƴan ta’adda da tsakiyar dare.

Adeniyi ya faɗi hakan ne a birnin Illorin yayin da yake gabatar da jawabi a jami’ar Illorin da ke jihar Kwara.

Rahotanni sun ce maharan sun farwa shingen binciken ababen hawa na tsaro da ke kusa da juna.

A nan ne kuma suka harbi jami’i guda sannan suka cinna wa ɗaya jami’in wuta da ransa.

Gwamnan jihar Kwara, AbdurRahman AbdulRazaq ya miƙa saƙon ta’aziyyarsa ga hukumar ta kwastam kan mutuwar jami’an biyu inda ya bayyana su a matsayin ƴan kishin ƙasa da suka rasa ransu yayin hidimta wa ƙasarsu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp