Home Taska Cutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara...

Cutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a Jihar

Yaran Fulani

Cutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a Jihar

 

Gwamnatin jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeriya ta ce babu gaskiya a rahoton ƙungiyar likitoci ta Médecins Sans Frontières, MSF, kan mutuwar ƙananan yara sakamkon cutar tamowa a jihar.

Wani rahoto da MSF ta fitar ya nuna damuwa kan ƙaruwar alƙaluman UNICEF da ke nuna cewa ana rasa kusan yara 30 cikin 100 ƴan ƙasa da shekara biyar a kowace rana sakamakon rashin abinci mai gina jiki, kuma kusan rabin mace-macen na faruwa ne a jihar Kebbi.

Sai dai kwamishinan yaɗa labarai na jihar Yakubu Ahmed, ya shaida wa BBC cewa gwamnati ba ta gamsu da ƙididdigar da aka fitar ba.

Gwamnatin ta kuma buƙaci MSF da UNICEF su gabatar da gamsassun hujjojin da za su tabbatar da rahoton saboda sun san abin da aka faɗa bai faru ba.

“Gaskiya muna taƙaddama da wannan ƙididdiga da suka bayar”. Idan hakan na faruwa, mu a matayin gwamnati ya kamata mu fara sani.”

“A ce yara suna mutuwa cikin ɗarurwa a kowace rana a jihar Kebbi ba tare da gwamnati ta sani ba, abin mamaki ne.Shi ya sa muke son su kawo mana shaida, dan mun san ba ta faru ba, babu wannan mutuwa da suka faɗa,” in ji shi.

Gwamnati ta kuma buƙaci su nemi afuwa kan kuskuren da suka yi, idan suka kaa gabatar da hujja.

“Ko su ba mu hujja, ko su ba da haƙurin cewa hakan bai faru ba.” in ji kwamishinan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp