Home Taska Cutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara...

Cutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a Jihar

Yaran Fulani

Cutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a Jihar

 

Gwamnatin jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeriya ta ce babu gaskiya a rahoton ƙungiyar likitoci ta Médecins Sans Frontières, MSF, kan mutuwar ƙananan yara sakamkon cutar tamowa a jihar.

Wani rahoto da MSF ta fitar ya nuna damuwa kan ƙaruwar alƙaluman UNICEF da ke nuna cewa ana rasa kusan yara 30 cikin 100 ƴan ƙasa da shekara biyar a kowace rana sakamakon rashin abinci mai gina jiki, kuma kusan rabin mace-macen na faruwa ne a jihar Kebbi.

Sai dai kwamishinan yaɗa labarai na jihar Yakubu Ahmed, ya shaida wa BBC cewa gwamnati ba ta gamsu da ƙididdigar da aka fitar ba.

Gwamnatin ta kuma buƙaci MSF da UNICEF su gabatar da gamsassun hujjojin da za su tabbatar da rahoton saboda sun san abin da aka faɗa bai faru ba.

“Gaskiya muna taƙaddama da wannan ƙididdiga da suka bayar”. Idan hakan na faruwa, mu a matayin gwamnati ya kamata mu fara sani.”

“A ce yara suna mutuwa cikin ɗarurwa a kowace rana a jihar Kebbi ba tare da gwamnati ta sani ba, abin mamaki ne.Shi ya sa muke son su kawo mana shaida, dan mun san ba ta faru ba, babu wannan mutuwa da suka faɗa,” in ji shi.

Gwamnati ta kuma buƙaci su nemi afuwa kan kuskuren da suka yi, idan suka kaa gabatar da hujja.

“Ko su ba mu hujja, ko su ba da haƙurin cewa hakan bai faru ba.” in ji kwamishinan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp